Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home JAKAR MAGORI

Ya Soke Abokinsa Da Wuka Har Lahira Akan Wayar ‘iPhone’

by Muhammad
February 4, 2021
in JAKAR MAGORI
2 min read
iPhone
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

An gurfanar da wani mutum mai suna Festus Stephen a gaban kotu bisa zargin daba wa abokinsa Abbas Mohammed Gudus wuKa har lahira bayan takaddama kan wayar ‘iphone’.

Stephen mai shekaru 27, ma’aikaci ne a ma’aikatar lafiya ta jihar Adamawa, hade da hukumar kula da lafiya a Mubi, an gurfanar da shi a gaban Mai Shari’a Helen Hammajoda da ke babbar Kotun na 2 da ke Yola, saboda kashe Abbas.

samndaads

Yana fuskantar tuhuma guda biyu, wadanda suka shafi cin hanci da rashawa, sabanin haka kuma za a hukunta shi a karkashin sashi na 1 (2) (b) na fashi da makami (Special Probidence) Dokar R11 ta dokokin tarayya, 2004.

A bayanin da ya yi na furci, Stephen ya ce, ya fara haduwa da Abbas ne a shekarar 2011, kuma tun daga wannan lokacin, suka zama abokai.

Wanda ake zargin ya kara da cewa, ya sayi iphone din wanda aka kashe a kan kudi Naira 40,000, kuma ya biya kudin gaba daya hannu-da-hannu, amma mamacin ya ki ba shi.

A cewarsa, ‘yan mintoci kadan bayan shan syrop dinsu na maye, marigayin ya fito da waya daga aljihunsa don yin kira. Yayin da yake kiran, wanda ake zargin ya fito da wuka ya daba masa a wuya.

Stephen ya ce, ya dauki wayar, ya tsoma hannayensa a aljihun mamacin ya dauki fakitin sigari, ya hau babur mai kafa uku ya fece ya gudu daga wurin, inda ya bar Abbas cikin jini.

An kai rahoton lamarin ga hukumar tsaro da abin ya shafa kuma daga karshe binciken ya kai ga cafke wanda ake zargi da kisan. An daga karar zuwa 24 ga Fabrairu 2021.

SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Wata Karamar Yarinya Ke Kashe Mutane Babu Ko Gezau

Next Post

An Cafke Direban Makaranta Saboda Lalata Da ‘Yar Shekara Hudu

RelatedPosts

Yadda Wasu Tsoffin Fursunoni Suka Sake Tafka Ta’asa

Yadda Wasu Tsoffin Fursunoni Suka Sake Tafka Ta’asa

by Sulaiman Ibrahim
5 days ago
0

Daga Mahdi M Muhammad A ranar Litinin da ya gabata...

An Damke Wani Dan Fashi A Nasarawa

An Damke Wani Dan Fashi A Nasarawa

by Sulaiman Ibrahim
5 days ago
0

Daga Mahdi M Muhammad Kakakin rundunar, ASP Ramhan Nansel, ya...

Makanike

Wani Mutum Ya Soke Makwabcinsa Da Kwalba

by Sulaiman Ibrahim
5 days ago
0

Daga Mahdi M Muhammad Rundunar ‘yan sandan reshen jihar Legas...

Next Post

An Cafke Direban Makaranta Saboda Lalata Da ‘Yar Shekara Hudu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version