Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Ya Zama Dole A Cike Gibin ‘Ya’ya Mata A Sashen Kiwon Lafiyar Arewa – Farfesa Binta  

by Muhammad
December 25, 2020
in LABARAI
4 min read
Mata
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba, Kaduna

 

samndaads

Farfesa Binta Abdulkareem, daya daga  cikin ‘ya’yan da su ka kirkiro da Kungiyar Kiwon Lafiya mai zaman kanta  wato Population  Reproductibe Health Initiatibe, ta yi kira ga Gwamnatin jihar Kaduna, nusamman da kuma sauran takwarorinta da ke a yankin Arewacin kasar da su  dinga bai wa horas da ‘ya’ya mata  kan ilimin kiwon lafiya domin a cike gibing da ake da shi na karkncinsu a yankin.

Binta  ta bayar da wannan shawarar ce a tattaunawar ta  da da manema labarai  a Kaduna kan aikin da kungiyar ta kirkiro da shi na horas da ‘ya’ya mata kan ilimin kiwon lafiya a daukacin jihohin da ke  yankin.   

 Binta, ta kuma jinjina wa Gwamnatin jihar  Kaduna kan daukar matakai wajen fara kafa damba kan shirin a shekara mai zuwa, inda ta ci gaba da cewa, ” Idan har bamu da ‘ya’ya mata a karkara da za su gudanar da aikin kiwon lafiya, musamman kan kiwon lafiyar mata,  wasu matan  ba za su iya fito  wa fili su fadi cuwukan da ke danunsu ba, domin a bisa al’adarsu, ba sa bukatar ma’aikacin  kiwon lafiya namji ya duba su ba”.

 In za’a iya tunawa, Kamfanin dillancin labarai na kasa NAN, ya ruwaito cewa, aikin  na  horas da ’ya’ya mata kan ilimin kiwon lafiya wato Girls for Health (G4H), an kirkiro da shi ne bisa nufin ciki gibin da ake da shi na karancin  ‘ya’ya mata a bangaren  ilimin kiwon lafiya da aka jima ana fama da shi a Arewacin Nijeriya.

 

 

Bugu da kari, aikin wanda ba a cikin akumma ake gudanar da shi ba, ana gudanar da shi ne, a makarantu Boko, inda kuma tuni, aka wanzar da aikin a wasu makarantu, an kuma faro aikin ne, a shekarar 2016 a jihohi hudu da su ka hada da, Kebbi, Sokoto, Jigawa da kuma Kaduna, wanda kuma Gidauniyar  Bill and Melinda gates ce ta ke daukar nauyi. 

Farfsa Binta  ta ci gaba da cewa, “Aikin  ya taimaka wa ‘ya’ya mata ‘yan makaranta da jimlarsu ta kai  375, inda hakan ya kai kashi 125 a cikin kashi dari, inda kuma wasu  113 tuni, aka samar ma su da guraben karatu a jami’oi da ban da ban kuma daga  ciki,  375 da su ka amafa, 113 tuni an samar ma su da guraben karatun a wasu jami’oi da ke kasar nan”.

 A cewar  Binta, “42  tuni, kuma sun samu guraben bayar da horo kan ilimin kiwon lafiya a wasu cibiyoyin bayar da horo kan ilimin kiwon lafiya, inda 22 su ka samu guraben karo ilimi, 28 kuma a Kwalejin Ilimin, 10 a makarantun kimiyya da fasaha wato polytechnic  11  kuma a sauran manyan makarantu”.

 Ta  bayyana cewa, daliban ‘ya’ya mata da su ka amfana, ma fi yawancinsu, ‘ya’yan marasa karfi ne kuma daliban ‘yan ajin karatu matakin sakandare na  SS2 ne, kuma duk munyi hakan ne bayan gudanar da bincike domin gano iya kokarinsu kafin bayar da daukin domin samar ma su da kyakyawan yanyi, samun horon tare da kuma wanzar da shirin  biyan kudin zana jarrabawarsu ta  WAEC da JAMB. 

 Binta ta ce, ” Mun gudanar da gasa tsakanin makaranta da makaranta, a karkashin aikinmu na horas da ‘yan makaranta ‘ya’ya mata  ga makarantu biyar tare da kaisu ziyara a wasu asibitoci, inda su ka koyi yadda kwararrun kiwon lafiya su ke gudanar da ayyukansu, yadda in sun koma cikin alumominsu za su iya bayar da taimako a fannin kiwon lafiya akalla a shekaru biyu, inda bayan sun zamo kwarrun jami’an kiwon lafiya za su taimaka sosai”.

Ta ce, ” Mun kuma gudanar da ginshikin bayar da horo kan ilimin kimiyya  domin kara ba su reno kan gudanar da gasar zana zama jarraba wa ko kuma zana jarrabawar aure, tare da kuma gudanar da bincike  domin tabbatar da alfanun aikin  kan kokarin daliban, inda ta kara da cewa, tare da goyon bayan aikin, hakan ya sanya wa iyayensu zimmar tura ‘ya’yansu mata zuwa makaranta domin su ma su kara jajirce wa wajen yin aiki tukuru domin fuskantar kalubalen da ke gabansu da kuma bai wa ‘yan baya kwarin gwaiwa.

 Binta ta yi kira ga ‘ya’ya mata ka da su fitar da rai, amma su tashi tukaru, wajen cimma mafarkansu, inda kuma ta yi kira ga iyaye da su ci gaba da kara wa ‘ya’yansu mata kwarin gwaiwa, musamman wajen neman ilimin kiwon lafiya yadda su ma za su bayar da ta su gudunmawar a fannin.

 A karshe, Binta   ta yi kira ga masu bayar da dauki a bangaren kwon lafiya ka da su gajiya wajen tallafa gwamnati, musamman wajen bai wa ‘ya’ya mata horo kan ilimin kiwon lafiya, inda ta kara da cewa, mun lura cewa, da aikin irin wannan, za a  kuma iya wanzar da shi a cikin alumma ganin cewa, za a Iya janyo shugabannin alumna domin amfanin ‘ya’ya mata da su kabfito daga gidajen marasa karfi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Tambuwal Ya Sa Hannu A Kasafin Kudin 2021

Next Post

Kirsimeti: Bishop Mamza Ya Raba Tallafin Dubu Goma-goma Ga Nakasassu A Adamawa  

RelatedPosts

Sojoji

Tsofaffin Sojoji Sun Nemi Karin Kudin Fansho

by Sulaiman Ibrahim
3 mins ago
0

Kungiyar tsofaffin sojoji ta kasa reshen jihar Anambra ta bukaci...

Ali Baba

Zaben Kananan Hukumomi: PDP Kwankwasiyya Ta Maka KASEIC A Kotu

by Sulaiman Ibrahim
19 mins ago
0

Bangaren Kwankwasiyya na jam'iyyar PDP a jihar Kano, ta jadadda...

Kurkuku

Binne ‘Ya Da Rai: Kotu Ta Yankewa Uba Hukuncin Kisa

by Sulaiman Ibrahim
28 mins ago
0

Babbar Kotun jihar Jigawa, da ke  garin Ringim ta yanke...

Next Post
Mamza

Kirsimeti: Bishop Mamza Ya Raba Tallafin Dubu Goma-goma Ga Nakasassu A Adamawa  

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version