Ya Zama Wajibi Sin Da Amurka Su Gina Alaka Da Juna Karkashin Salon Martaba Juna Da Daidaito
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Zama Wajibi Sin Da Amurka Su Gina Alaka Da Juna Karkashin Salon Martaba Juna Da Daidaito

byCMG Hausa
2 years ago
Amurka

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya ce ya zama wajibi kasashen Sin da Amurka su gina alaka bisa salon martaba juna da daidaito, da girmama bambance-bambancensu na tarihi, da al’adu, da tsarin zamantakewa da hanyoyin ci gaba. Kaza lika ya wajaba sassan biyu su kare moriya, da manyan abubuwan da ke jan hankalin su.

Wang Wenbin, wanda ya bayyana hakan a Juma’ar nan, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, ya ce wasu rahotanni sun ruwaito cewa, a ranar Laraba, fadar White House ta Amurka ta shaidawa manema labarai shirin sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken, na ziyartar kasar Sin, inda aka bayyana cewa, Amurka na aiwatar da manufofin cudanya da kasar Sin masu dorewa, wato salon dangantakar sassan biyu yana kunshe da takara ba wai neman tashin hankali, fito-na-fito, ko sabon salon cacar baka ba.

  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Gimama Mabambantan Wayewar Kai Ta Bil Adama

Kaza lika Amurka na fatan ci gaba da gudanar da takara mai tsafta. Za ta kuma yi kokarin daidaita yanayin takara tare da Sin, da kuma bunkasa hadin gwiwa kan batutuwan da suka dace da burikan su.

Da yake amsa tambayar da aka yi masa kan wannan batu, Wang Wenbin ya ce shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sha nanata cewa, bai dace alakar Sin da Amurka ta zama ta idan bangare daya ya samu dayan ya yi asara ba, maimakon haka, dacewa ya yi sassan biyu su rika cimma nasara tare, ta yadda kowa zai iya samun riba ko hasara.

Ya ce ya kamata Sin da Amurka su rika kallon juna a matsayin abokan tafiya, a manufofin su na gida da na waje, da aiwatar da manyan tsare-tsare bisa ka’idoji, da nacewa martaba juna, da tafiya tare, bisa zaman lafiya da hadin gwiwar cimma moriyar juna. Kana su lalubo hanya mafi dacewa ta kyautata jituwa tsakanin su. Hakan ne zai kare moriyar su, da ma irin fata da sassan kasa da kasa ke yi musu.

A wani ci gaban kuma, kamfanin tsaron yanar gizo na Amurka mai suna “Mandiant Corporation”, ya fitar da wata sanarwa a baya-bayan nan, wadda a cikin ta ya ce, yana zargin kasar Sin da baiwa wasu masu kutsen yanar gizo goyon baya, inda suka yi kutse cikin daruruwan na’urori masu kwakwalwa na gwamnati, da na sassa masu zaman kan su dake kasashe daban daban.

Da yake amsa tambaya game da hakan, Wang Wenbin ya ce da ma wannan kamfani ya sha fitar da irin wadannan rahotanni na karya, game da wadanda yake kira da wai “masu kutsen yanar gizo na Sin”, kuma abubuwan dake kunshe cikin rahoton kamfanin ba kamshin gaskiya ko kwarewar aiki a cikin su. (Saminu Alhassan)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Kokarin Tinubu Wajen Inganta Rayuwar ‘Yan Nijeriya Bayan Cire Tallafin Mai

Kokarin Tinubu Wajen Inganta Rayuwar 'Yan Nijeriya Bayan Cire Tallafin Mai

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version