Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home WASANNI

Yadda Aka Fafata Tsakanin Chelsea da Liverpool

by Muhammad
March 5, 2021
in WASANNI
2 min read
Chelsea
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ta ziyarci abokiyar hamayyarta wato kungiyar kwallon kafa ta Liverpool domin buga wasan Premier League karawar mako na 29 da suka fafata a filin wasa na Anfield ranar Alhamis.

A wasan farko da suka buga a kakar bana, Liverpool ce ta doke Chelsea 2-0 a Stamford Bridge ranar 20 ga watan Satumba kuma yanzu Chelsea tana mataki na biyar a kan teburin Premier League da maki 44, ita kuwa Liverpool mai maki 43 ita ce ta shida.

Liverpool tana da mai koyarwa Jurgen Kloop dan kasar Jamus, itama Chelsea mai Thomas Tuchel dan Jamus ne sannan kuma masu horarwar sun fafata a junansu sau 14 a tsakaninsu, inda Kloop ya yi nasara a wasa tara da canjars uku, Tuchel ya ci wasa biyu.

Karawa a tsakaninsu:

Liverpool za ta iya cin wasa na biyar a jere a kan Chelsea a karon farko tun bayan 1972/73 kuma wasa daya kacal Chelsea ta yi nasara a kan Liverpool a fafatawa 12 baya a Premier da canjaras uku aka doke ta fafatawa shida har ila yau Chelsea ta sha kashi sau 23 a gasar Premier League a hannun Liverpool, kungiyar da ke kan gaba a doke ta a Ingila.

Kwazon Liverpool:

Liverpool ta yi rashin nasara wasa hudu a jere a Premier League a gida a bana kuma watakila ta sha kashi a karo na biyar a jere a Anfied da zai zama na farko a tarihin kungiyar saboda karawar karshe da Liverpool ta yi nasara a gida a kakar nan, ita ce ranar 16 ga watan Disamba da ta doke Tottenham 2-1 har ila yau Chelsea ba ta yi nasara a kan Jurgen Kloop a wasa biyar din farko a lig a gida ba, inda ya yi nasara a fafatawa biyu da canjaras uku.

Kwazon Chelsea:

Thomas Tuchel ya ja ragamar wasa tara a Chelsea ba a doke shi ba a dukkan fafatawa, inda ya ci karawa shida da canjaras uku kuma Chelsea ta zura kwallo 10 a raga tun bayan da Tuchel ya karbi aiki a watan Janairu aka ci kungiyar ta Stamford Bridge guda biyu kawai.

Manchester City ce kan gaba wajen hada maki a Premier League, sai Chelsea da ta biyu da ta samu 15, tun bayan da Tuchel ya koma kungiyar sannan Tuchel bai ci wasa bakwai da ya ziyarci takwaransa Kloop ba, inda ya yi canjaras biyu da rashin nasara biyar a wasannin waje.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ronaldo Ya Sake Kafa Sabon Tarihi

Next Post

Nijeriya Ta Fara Shirin Buga Wasa Da Kasashen Benin Da Lesotho

RelatedPosts

Leicester

Leceister City Ta Je Wasan Karshe A Kofin FA Bayan Shekara 52

by Muhammad
3 hours ago
0

Kungiyar kwallon kafa ta Leicester City ta kai wasan karshe...

Juventus Ta Sake Samun Koma Baya A Siriya A  

by Muhammad
3 hours ago
0

Kungiyar kwallon kafa ta Juventus ta sake samun koma baya...

Getafe

Akwai Gajiya A Jikin ‘Yan Wasana Lokacin Fafatawa Da Getafe – Zidane

by Muhammad
3 hours ago
0

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid, Zinadine Zidane, ya...

Next Post
Nijeriya

Nijeriya Ta Fara Shirin Buga Wasa Da Kasashen Benin Da Lesotho

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version