Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

Yadda Aka Gudanar Da Bikin Dashen Shuka Itace A Jami’ar ABU Zariya

by Tayo Adelaja
September 16, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Idris Umar, Zariya

A ranar alhamis din da ta gabata ne Hukumar Jami’ar ABU Zariya ta yi bikin dashen itatuwa na shekarar 2017, tare da gudanar da taron karawa juna sani kan muhimmacin dasa itace da kuma illar sare shi ga rayuwar bil’Adama.

Taron dai an gudanar da shi ne babban dakin taro na Jami’ar wato Assembly Hall da ke a harabar jami’ar, inda aka gabatar da kasidu da suka shafi muhimmanin dashen itacen.

Cikin malaman da suka gabatar da kasidun akwai Farfesa Jibril Jibril, Daraftan (Center for Dryland) na jami’ar Bayaro, Kano, sai shaharanren masanin harkar kimiyyar dazuka da shuka itace, Cif Giwa Radife  na (Pribate Forest Demonstrtion Plantation).

Wadanda suka gabatar da kasidun sun fitowa da mahalarta taron wasu sirruka da ke cikin dasa itatuwa don samun iska mai kyau ga rayuwar al’ummar a duniya baki daya.

Da yake karanta nasa jawabin, Farfesa Kabir Bala, wanda ya wakilci Shugaban ABU, Farfesa Ibrahim Garba, ya ce wa, Farfesa Kabir ya bi sahun shugabannin jami’ar da suka shude wajen jajircewa don ganin an ci gaba da taron dashen shuka duk shekara, kuma ya nuna cewa, dole ne a tashi tsaye don tunkarar duk matsalolin da ake samu a sakamakon sakaci da ake yi na dashen itatuwa a duk fadin Nijeriya.

Ya ce duk da matsalar da jami’ar take da shi na rashin kudi, takan dage wajen raya tarukan dashen itatuwa a duk shekara saboda tunawa da Nijeriya.

Farfesan kuma ya gargadi al’umma da su guji sare itace ba gaira babu dalili. Ya ce, idan wani dalili yasa an sare, to a shuka wani akan lokaci don ya maye gurbin wanda aka sare.

Ya kuma nuna irin hadarin da duniya ke fuskanta a sakamakon rashin wadatattun itatuwa masu sarrafa iska a dangantakar mutane da sararin samaniya. Ya ce, da yawan manyan guguwa da ake fama da ita ko kuma ambaliyar ruwa, suna faru ne dalilin karancin itatuwa a doron kasa. Saboda haka ce al’umma su tashi tsaye a marawa tsarin dashen shuka itatuwa a duk fadin kasar nan.

A nasa bangaren, wakilin Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru el-Rufa’i, Shugaban Hukumar Kula da Muhalldi, Malam Yusif Abdullahi, ya ce gwamnatinsu na bada gagarumar gudunmawa wajen dasa itatuwa, domin kowace shekara ana dasa itatuwa milyan biyu a fadin jihar.

Har ila yau, ya gabatar da sakon Gwamna el-Rufa’i na bukatar da yake da ita na a ba shi hadin kai domin dasa a duk fadin jihar. A cewarsa, gwamnan ya ji dadin wannan taro da ake gabatarwa, kuma yana fatan zai dore kamar yadda aka tsara.

Shi ma tsohon shugaban jami’ar ta ABU Farfesa Shehu Usman Abdullahi ya yaba matuka ga tsarin gudanarwa jami’ar a hannunta jagoranta na yanzu, inda ya ce duk mutumin da ya ci gaba da irin wannan aiki, ya nunawa duniya cewar ya san darajar halitta a doron kasa.

Shugaban taron Dakta S.K Musa ya nuna jin dadinsa tare da yabo ga sarakuna da dagattai da jami’an tsaro da suka sami damar halattar taro, kuma ya yi roko ga duk wadanda aka ba su itaciya da su daure su shuka, kar su ajiye ta a gida ta lalace.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwa Na Cigaba Da Janyo Asarar Rayuka A Kebbi

Next Post

An Goyi Bayan Gwamnatin Tarayya Kan Yaki Da Rashawa

RelatedPosts

Kasuwa

An Yi Kira Ga ‘Yan Kasuwa Su Rangwanta Wa Al’umma A Watan A Zumin Ramadan

by Muhammad
12 hours ago
0

Daga Alhussain Suleiman, Yayin da al’ummar musulmin Duniya suka fara...

Dalibai

Garkuwa Da Ake Yi Da Dalibai Yaki Ake Da Yankin Arewacin Kasar Nan, Inji Gambo Danpas

by Muhammad
12 hours ago
0

Daga Alhussain Suleiman, Garkuwa da ake yi da daliban a...

Kiwon Lafiya

Shugaban Makarantar Fasahar Kiwon Lafiya Na Kano Yana Ayyukan Da Ke Kare Kimar Gwamna Ganduje–Dokta Amina Ganduje.

by Muhammad
12 hours ago
0

Daga Ibrahim Muhammad, A irin ayyukan jinkai da mutane suke...

Next Post

An Goyi Bayan Gwamnatin Tarayya Kan Yaki Da Rashawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version