Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

byBello Hamza
2 weeks ago
Taron

A ranar Asabar na makon jiya ne Cbiyar Yusufu Bala Usman ta shirya taron masana da suka fito daga sassan kasar nan inda suka gabatar da mukala daban daban a kan irin rayuwa da gwagwarmayar da Marigayi Dr Bala Usman ya yi a lokacin rayuwarsa, ya kuma rasu ne shekara 20 da suka gabata.

Cikin shahararrun masanan da ke kan gaba wajen gabatar da bayanai a wajen taron sun hada da Farfesa Attahiru Jega, Farfesa Iyochia Ayu, Farfesa Jerome da kuma Dr Auwalu Anwar da Ambasada Abdul Zango.

  • Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
  • Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

Bayanan nasu ya fito da irin gudummawar da Bala Usman ya bayar ne a cikin littatafan da ya rubuta da kuma akidojinsa na yadda ya kamata a tafiyar da rayuwar al’umma cikin nasara.

A nasa tsokacin Dr Auwalu Anwar ya ce, lallai da Bala Usman zai dawo duniya a yanzu bayan shekara 20 da rasuwarsa da zai nuna bacin ransa a kan irin kungiyoyin siyasar da muke dasu a Nijeriya. Ya kara da cewa, Bala Usman yana mai fatan samun jami’iyyun siyasa da suka samu asali ne daga kokari da fafutukar talakawa, sune kuma suke gudanar da ita ba manyan masu kudi ba wadanda ke amfani da jami’iyyun domin kaiwa ga madafun iko.

Shi kuwa Ambasada Abdul Zango ya bayyana irin gudummwar da Bala Usman ne ya bayar wajren samar wa kasar nan alkiblar yadda za ta tafiyar da harkokin hulda da kasashen waje. Ya ce marigayi Bala Usman ne ya rubuta wa marigay shugaban mulkin soja na kasar nan Murtala Mohammed jawabin da ya yi a taron kungiyar kasashen Afrika ta OAU wanda ya gudana a kasar Addisa Baba, jawabin da ya shahara a duniya. Ya kuma bayyana cewa, in har da Bala Usman zai dawo ya ga yadda ake tafiyar da harkokin kasashen waje na Nijeriya a halin yanzu lallai ba zai ji dadi ba saboda yadda ake tafiyar da it ba tare da kishin kasa da akida ba.

Daga karshe,mahalarta taron sun meni a samar da wata kungiya da za ta jagoranci isar da sakon akidojin Bala Usman ga al’umma domin bai kamata a bar irin wannan kyawawan fata na Bala Usman su tafi a banza ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

May 23, 2025
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

April 18, 2025
Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya
Kananan Labarai

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

April 5, 2025
Next Post
Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version