Yadda Aka Kashe Mutum Shida Da Sace Wasu Ranar Sallah A Sokoto
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Kashe Mutum Shida Da Sace Wasu Ranar Sallah A Sokoto

byRabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Sallah

Akalla mutane shida ne rahotanni suka ce an kashe tare da yin garkuwa da mutane sama da 100 yayin da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai wa wata al’umma hari a Jihar Sokoto.

Rundunar ‘yansanda sa Jihar Sokoto, ta bakin mai magana da yawunta, Ahmed Rufa’i, ta tabbatar da kashe mutum sama da 6 tare da yin garkuwa da dama a Tudun Doki da ke Karamar hukumar Gwadabawa a Sokoto.

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Kare Muhalli A Wuraren Kewayen Rawayen Kogi
  • Rashin Wadatar Kayan Aiki: Yadda Nijeriya Ta Kasa Dakatar Da Asarar Naira Tiriliyan 1.4 A Sashen Kiwon Lafiya

Rufa’i ya ce duk da cewa har yanzu ana tattara bayanai game da harin, amma an tabbatar da mutuwar mutum shida.

A cewarsa, jami’in ‘yansandan shiyya da ke Gwadabawa ya jagoranci tawagar ‘yansanda zuwa al’umma domin duba lamarin tare da dawo da zaman lafiya.

Akalla mutum shida ne rahotanni suka ce an kashe tare da yin garkuwa da mutane sama da 100 yayin da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai wa wata al’umma hari a Jihar Sokoto.

“Rundunar bincike ta gano gawarwaki shida kuma ana ci gaba da kokarin kwato sauran mutanen da suka bata,” in ji kakakin ‘yansandan.

A cewar mazauna kauyen, maharan wadanda adadinsu ya kai kusan bakwai, sun far wa al’ummar da misalin karfe 1:30 na safe dauke da manyan bindigogi, sun harbin kan mai uwa da wabi inda suka yi awon gaba da ’yan uwa da dama.

Gwadabawa, daya daga cikin kananan hukumomin da ke Gundumar Sanata ta Gabas ta Jihar Sakkwato, ta kasance cikin kwanciyar hankali har zuwa harin da aka kai.

A halin da ake ciki dai sojojin Operation Whirl Punch sun ci gaba da kai samame tare da sintiri a Jihar Kaduna inda suka kashe wasu ‘yan bindiga uku a hanyar Gonna Rogo-Eka a Karamar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna.

Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida da Harkokin Gida Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Majiyarmu ta ruwaito cewa, a ranar 14 ga watan Yuni, sojojin sun kashe ‘yan bindiga 36, ciki har da Buhari Alhaji Halidu, wanda aka fi sani da “Buharin Yadi,” daya daga cikin manyan ‘yan fashin da suka addabi Arewa.

Bayan kashe-kashen, mazauna yankunan kan iyakar Kaduna da Katsina sun shiga cikin farin ciki.

A wani samame na baya-bayan nan, kwamishinan ya ce, “Dakarun da ke aikin sintiri sun kashe ‘yan bindiga uku a yankin Gonna Rogo-Eka na Karamar Hukumar Kajuru.”

Ya kara da cewa an kwato bindigogin AK-47 guda biyu, kwanson AK-47 guda hudu da harsashi 81 na 7.62mm bayan wani kazamin fada aka gwabza da ‘yan fashin.

“Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce sojojin sun gudanar da sintiri na musamman a yankin inda suka samu ‘yan bindigar. Bayan musayar wuta, an kashe uku daga cikin masu laifin a takaice.

Gwamna Uba Sani, da yake magana a kan ci gaban, ya gode wa jami’an tsaro tare da yaba wa dakarun da ke karkashin jagorancin babban kwamandan runduna ta daya ta sojojin Nijeriya, Manjo Janar M.L.D Saraso, kan yadda suka kara kaimi wajen ganin an gudanar da bukukuwan Sallah lami lafiya. ‘yan kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Babban Burina Na Ga Ina Taimaka Wa Mata ‘Yan’uwana – Garkuwar Matan Giwa

Babban Burina Na Ga Ina Taimaka Wa Mata ‘Yan'uwana - Garkuwar Matan Giwa

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version