Yadda Ambaliya Ta Lalata Gidaje 255 A Garin Natsinta Da Ke Katsina
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ambaliya Ta Lalata Gidaje 255 A Garin Natsinta Da Ke Katsina

byEl-Zaharadeen Umar and Sulaiman
1 year ago
Natsinta

Mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a kauyen Natsinta cikin karamar hukumar Jibiya da ke Jihar Katsina ya lalata gidaje kimanin 255, jim kadan bayan dauke ruwan sama.

Lamarin ya faruwa ne sakamakon ruwan sama da aka rika yi ba kaukautawa kwanaki a jere, wanda ya yi sanadiyar korar mutane fiye da dubu daya daga muhallinsu, wanda da yawansu mata ne da kananan yara.

  • PCACC Ta Kama Shugabannin Ƙananan Hukumomi 3 Bisa Zargin Almundahanar Miliyan 660
  • Gwamnatin Kano Za Ta Tsara Zamantar Da Magungunan Gargajiya

Sai dai ba a samu labarin rasa rai ba, amma dai mutane da dama sun samu raunuka, wanda yanzu haka suna asibiti suna karbar magani.

Haka kuma mafiyancin gidajen da ruwa ya ruguje gidajen kasa ne wanda a dalilin haka jama’a da dama sun rasa matsugunnisu kuma suna bukatar taimakon gaggawa.

Mai unguwar garin Natsinta, Malam Dayyabu ya nuna fargaba kan faruwar wannan lamari, inda ya ce yanzu abin da ke gabansu shi ne, kokarin samun abin da za su sanya a bakin salati tun da ruwa ya hargitsa duk abubuwan da suke da shi.

“Babu abin da zan ce sai dai mun gode Allah wanda ya kaddara faruwar wannan lamari kuma babu wanda ya isa tambayi dalilin me ya sa, ganin damarsa ce ya yi haka,” in ji mai unguwa.

A cewarsa, kimanin gidaje 250 iftila’i ya shafa, ba a maganar gidajen da ruwa ya kada a yau (Litinin), yanzu haka wasu karin gidaje guda 4 sun kara faduwa sannan kuma wasu guda biyu sun ruguje baki daya.

“Muna kira ga gwamnatin Jihar Katsina karkashin Gwamna Malam Dikko Umar Radda da su taimaka wa al’umma da kayayyakin rufi da katifu da siminti da bulo da kudadai domin su samu inda za su tsugunna su yi barci a yanzu, ” in ji shi.

Sai dai kuma dan majalisar dokoki mai wakiltar karamar hukumar Jibiya Honarabule Mustapha Yusuf ya ziyarci kauyen Natsinta domin jajanta masu da ganin irin barnar da ruwan ya yi, inda ya yi alkawari kai kokensu a gaban majalisa domin tattauna yadda gwamnati za ta tallafa wa wadanda wannan bala’i ya shafa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Next Post
Martani: Ba Hannuna A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa – Hon Boza

Martani: Ba Hannuna A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa - Hon Boza

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version