Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ambaliya Ta Yi Barna A Wasu Gonakin Shinkafar Taraba

by
2 years ago
in NOMA
2 min read
Yadda Ambaliya Ta Yi Barna A Wasu Gonakin Shinkafar Taraba
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Sharhi: Rashin Karfafa Noman Auduga Tamkar Kamun Gafiyar Baidu Ne Ga Nijeriya

Noman Rogo: Yadda Nijeriya Ke Asarar Naira Tiriliyan 27 A Kasuwar Duniya

Wasu daga cikin manoman shinkfa a jihar Taraba bana baau ji dadin noman ta ba a bana, musamman ganin yadda zaiyi wuya su samu wata babbar riba ko amfani mai yawa da auka saba samu a duk ahekara in sun noma shinkafar.
Hakan ya biyon yadda ambaliya ta yi barna a gonalan waau manoman dake shuka shinkafar.
Ambaliyar ruwa ta lalata daruruwan gonakin shinkafa a kananan hukumomin Gassol da Bali da ke Jihar Taraba.
Gonakin shinkafar wadanda suke a gefen Kogin Taraba dukkansu ruwa ya mamaye su tare da haifar wa manoma hasarar miliyoyin naira.
Rahotanni sun nuna cewa, wuraren da barnar ta fi muni su ne, yankin Bali da Tella da Sardirde; inda dubban manoman shinkafar suka yi hasarar shinkafa wadda ke gab da nuna.
A cewar wani manomi a yankin, Yakubu Yuguda, ya shuka buhunan shinkafa uku kuma ya kiyasta cewa zai samu sama da buhunan shinkafa 120, amma ambaliyar ruwar ta lalata gonarsa bakidaya.
Ya ci gaba da cewa, manoma sama da 50 da ke yankin Tella, su ma ambaliyar ta lalata gonakinsu.
Yakubu ya kara da cewa wadansu da suka yanke shinkafarsu, ruwa ya yi awon gaba da shinkafar kafin su gyara ta.
Bugu da kari, rahotani sun nuna cewa, dubban manoman na shinkafar su na noma ta ne a gabar Kogin Taraba mai tsawon kimanin kilomita 300 kuma ambaliyar ta mamaye daukacin gonakin da ke gabar kogin.
Shi kuwa wani manomin shinkafar Malam Bello Maigari, ya sanar da cewa a yankinsu na Sardirde dubban manoman shinkafa sun yi hasarar shinkafar wadda ke ganiyar nuna a sanadiyyar ambaliyar ruwan.
A cewar Yakubu, yankin na samar da shinkafa mai yawan gaske a duk shekara a jihar, inda ya kara da cewa, amma wannan matsalar ta ambaliya za ta haifar da karancin shinkafa a bana a jihar.
Ya ci gaba da cewa, akasarin manoman shinkafar da ruwa ya lalata gonakinsu sun karbi bashi ne don noma shinkafar, ga shi ruwa ya lalata ta.
Ya yi kira ga gwamnatin jihar ta taimake musu da tallafi domin samun saukin radadin asarar da su ka tabka.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

“A Na Shigo Da Albasa Tan Miliyan Daya Nijeriya Duk Shekara”

Next Post

Masu Kiwon Zuma A Abuja Sun Amfana Da Kwangin Zuma 300

Labarai Masu Nasaba

Sharhi: Rashin Karfafa Noman Auduga Tamkar Kamun Gafiyar Baidu Ne Ga Nijeriya

Sharhi: Rashin Karfafa Noman Auduga Tamkar Kamun Gafiyar Baidu Ne Ga Nijeriya

by Abubakar Abba
1 week ago
0

...

Rogo

Noman Rogo: Yadda Nijeriya Ke Asarar Naira Tiriliyan 27 A Kasuwar Duniya

by Abubakar Abba
2 weeks ago
0

...

Gurjiya

Sirrin Noman Gurjiya Wajen Bunkasa Tattalin Arziki

by Abubakar Abba
3 weeks ago
0

...

Bunsuru

Kiwon Bunsuru A Saukake

by Abubakar Abba
1 month ago
0

...

Next Post
Masana Sun Yi Gargadi Kan Karancin Kudan Zuma A Nijeriya

Masu Kiwon Zuma A Abuja Sun Amfana Da Kwangin Zuma 300

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: