Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bayar Da Taimakon Gyaran Makabartu Ya Ci Tura A Kano

by
2 years ago
in RAHOTANNI
2 min read
Dala
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

Babu shakka masu kula da makabartu a nan Jihar Kano su na bakin kokarinsu karkashin kwamatin gyaran makabarta, a wani locacin kuma ana dora laifin kan gwamnati, dalili kuwa shi ne samar da kwamati guda a kan gyaran duk makabartar data lalace wannan ya sa mutane su ka zuba ido kawai gwamnati ta yi musu gyaran duk makabartar da ta lalace, wannan ba karamin kuskure ba ne, domin wancan kwamiti na kula da duk makabartar Jihar Kano sai fa an bashi zai zo ya yi aikin da ya kamata a duk makabarta, amma mutane sun manta cewa  wannan guri ne da kowa nan za a kai shi  .

Zan yi magana a kan al’ummar Jihar Kano da ma na wasu jihohin a kan makabartunmu, abin na ke so na ce shi, Allah ya azurta mu da masu kudi da dama, ku fidda ranku cewa wai gwamnati sai ta zo  ta gyara muku makabartunku. Wannan lokaci ne na damuna, idan ka je ka shiga duk makabartar dake yankinmu na Arewa zaka ga abin ta kai ci kuma wannan lalacewar bata gagari mutanen yankin su yi maganin ta ba, akwai mutum daya wanda zai iya ba da gudunmawar tifa 50 kuma bai girgiza ba, duk matsalar makabarta abin da yake da munta shi ne zaizaya ko idan an yi ruwa kabari ya rufta, amma wannan taimakon sai ya gagara, bayan makabartar nan tabbas  idan ka mutu nan fa za a kai ka, amma wannan taimakon ya gagara, kowa ya na jiran gwamnati ta zo ta gyara.
To, a gaskiya kirana ga  al’umma mu sake tunani  domin duk makabarta ta kowa ce  mu hadu mu gyara domin na tabbata yanzu da al’ummar ko wacce unguwa za su bayar da tallafin ko da Naira 50 ce kawai, to za a sha mamaki irin kudin da za a tara wajen gyaran makabartar a ko wanne yanki. Mu daina cewa muna jiran gwamnati ta zo ta yi mana, domin abubuwa sun canja.
A yi taimakon kai da kai shi ya kamata mu sa a gaba domin yanzu babu wani da zai saurari kukan duk wani kwamiti dake neman tallafin gyara makabarta, saboda yanzu babu mai neman mukamin komai a wajan talakawa sai nan gaba ka dan idan wani zabe ya matso za ka ji kai tallafi iri-iri, domin lokacin bukatarsu ya zo wasu daga cikinsu ke nan.
Kirana ga masu wadata wanda su ke neman lada domin zuwa gobe ranar lahira su dauka su je makabartun da ke fadin Jihar Kano akwai wanda lalacewar abin ta kaici ne kwarai da gaske za su ga kabari a waje ko a kusa da ruwa ko da yaushe ruwa yana iya tafiya da shi Allah ka tsare mu.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Mun Yi Murna Da Allah Ya Dawo Mana Da Diyarmu Sa’adiyya – Iyayenta

Next Post

Ku Kawo Karshen Ta’addanci A Bauchi – Gwamna Bala Ga Hukumomin Tsaro

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

by Ahmed Muhammad Dan'asabe
1 day ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

by
2 days ago
0

...

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

by CMG Hausa
2 days ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

by
3 days ago
0

...

Next Post
Taki

Ku Kawo Karshen Ta’addanci A Bauchi – Gwamna Bala Ga Hukumomin Tsaro

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: