Yadda Ci Gaban Kasar Sin Ke Tasiri A Duniya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ci Gaban Kasar Sin Ke Tasiri A Duniya

bySulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Sin

Idan muka ce duniya baki daya ta bibiyi sanarwar cikakken zaman taro karo na 3 na kwamitin kolin JKS karo na 20 ba mu yi karya ba. Magoya baya da abokan huldar Sin sun kasa kunne su ji tabbacin labarin kwanciyar hankali da daidaiton tsarin ci gaban kasar, yayin da masu sukar lamirin kasar suka yi ta kokarin gano alamun karuwar matsaloli, da damuwa, ko ma yiwuwar rarrabuwar kawuna tsakanin shugabannin JKS. A karshe dai, magoya baya sun samu dalilan da suka kwantar musu da hankali, kuma masu zagi dole ne su kasance cikin takaici. A bayyane, zaman ya nuna ci gaba a tsarin siyasa, da tattalin arziki da zamantakewa da aka tsara a babban taron JKS karo na 20 da aka gudanar a shekarar 2022. Zaman ya mayar da hankali ne kan al’amuran cikin gida da nufin kammala aikin zamanantarwa bisa tsarin gurguzu nan da shekarar 2035, da gina ingantacciyar hanyar tattalin arziki ta gurguzu da kuma zamanantar da tsarin kasar da iya tafiyar da harkokin mulki.

Mu dubi tsarin kasuwancin duniya na wannan zamani, jimillar kayayyakin shige da fice na kasar Sin ya kai kusan dalar Amurka tiriliyan 6, lamarin da ya sa kasar Sin ta kasance babbar abokiyar cinikayya ga kasashe fiye da 120. Kasar Sin tana da fiye da rabin sabbin motocin lantarki da aka sayar a duk duniya a yau, kuma tana daukar sama da kashi 80 cikin 100 na kayayyakin samar da wutar lantarki bisa hasken rana a duniya. Yana da wuya a yi tunanin kasuwannin duniya na kwamfutoci da na’urorin laturoni, da sinadarai na hada magunguna, da injuna, da motoci, da sauran kayayyaki daban-daban ba tare da tabo rawar da kasar Sin ta taka ba.

Kusan shekaru 100 da suka shige, tsohon shugaban Amurka Franklin D. Roosevelt ya bayyana cewa, “Yadda matsayinmu a tarihi ke cike da haske haka yake da hadari. Ko dai duniya ta karkata zuwa ga ci gaba da hadin kai da wadatar arziki a ko’ina, ko kuma ta rarrabu.” Wannan gaskiya ne a shekarun 1930s kuma ba shakka haka lamarin yake a zamaninmu na yau. Dukkanmu masu ruwa da tsaki ne wajen samun nasarar ci gaban tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin saboda hakan na da matukar tasiri ga tattalin arzikin duniya. Kuma wadanda ke yi wa Sin munanan fata harbin kansu kawai suke yi a kafa. (Mohammed Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Sojoji Sun Ceto Wata Ƴar Chibok, Sun Miƙa Ta Ga Gwamnatin Borno

Sojoji Sun Ceto Wata Ƴar Chibok, Sun Miƙa Ta Ga Gwamnatin Borno

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version