Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al'umma A Kagara – Rahoto
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto

bySadiq
3 years ago
'Yan Bindiga

Wani rahoto da kafar yada labarai ta PRNigeria ta fitar ya nuna cewa hare-haren da ake kai wa al’ummar Chonoko a jihar Kebbi, da kuma al’ummar Kagara a jihar Neja sun taimaka matuka gaya wajen raguwar kwararrun likitocin kiwon lafiya, da ayyukan ilimi, da sauran ayyukan jin kai a jihohin.

Baya ga kalubalen rashin tsaro da ake fama da shi, rahoton ya yi nuni da cewa, rayuwa a sansanonin ‘yan gudun hijirar ta zama abu mai wahala, ganin yadda jama’a ke matukar bukatar manyan ababen more rayuwa na dan Adam kamar abinci, ruwa, matsuguni da dai sauransu. .

  • Sojoji Sun Cafke ‘Yan Bindiga 7, Sun Kubutar Da Wasu Mutane
  • Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

Sai dai kafar yada labaran ta zargi masu ruwa da tsaki a jihar da yin sama da fadi da kayan agajin da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayar ga al’ummomin da ba su da karfi.

Wakilin PRNigeria, Mukhtar Madobi ne, ya bayyana hakan a yayin wani taron bita na yini biyu a Abuja mai taken: ‘Yan Jarida na Jin kai don Ci gaban Tattalin Arziki’ a lokacin da yake gabatar da wani bincike kan halin jin kai da kuma halin da ‘yan gudun hijira ke ciki a jihohin Kebbi da Neja.

Ya yi nuni da cewa ilimi wani bangare ne mai matukar muhimmanci wanda shi ma yake fama da matsalar rashin tsaro.

Sakamakon binciken ya nuna cewa an rufe akasarin makarantu a kauyukan saboda fargabar hare-haren ‘yan bindiga.

“Manoma a wasu kauyukan da ke kusa da su sun koma biyan haraji ga ‘yan bindiga domin samun damar shiga gonakinsu da gudanar da ayyukan noma. Duk da haka, ayyukan noma sun ragu sosai ta yadda hakan ya haifar da karuwar matsalar karancin abinci.

“Yawancin makarantun kauyukan a rufe suke saboda fargabar hare-haren ‘yan bindiga, wanda hakan ya shafi fannin ilimi a yankin.”

Rahoton ya kara da cewa, “Yanzu haka harkar kiwon lafiya an mata kisan mummuke, saboda Babban Asibitin garin ba ya aiki yadda ya kamata saboda fargabar ‘yan bindiga.”

A halin da ake ciki, wasu asibitocin da ke cikin garuruwan an mayar da su sansanonin ‘yan gudun hijira inda ake kula da wadanda abin ya shafa.

Ya koka da yadda lamarin ya sa dalibai da dama daina zuwa makarantu, wanda hakan ya kara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a yankin da ma kasar baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
Tsadar Man Dizil Na Barazana Ga Masu Kiwon Tarwada A Edo

Tsadar Man Dizil Na Barazana Ga Masu Kiwon Tarwada A Edo

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version