Yadda Karyewar Darajar Naira Da Cire Tallafin Mai Suka Durkusar Da Masana’antun Kasar Nan
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Karyewar Darajar Naira Da Cire Tallafin Mai Suka Durkusar Da Masana’antun Kasar Nan

byBello Hamza
1 year ago
Naira

Janye tallafi man fetur da aka yi a kwanan nan da kuma karya darajar naira sun shafi manya da kananan masana’atu da dama a Nijeriya, wanda hakan ya kai ga raguwar kudaden shiga da kuma matsalolin da suka shafi kudade gudanarwa.

Tunda aka janye tallafin mai a ranar 29 ga watan Mayu a shekarar 2023, farashin man fetur ta tashi kashi fiye da 193 abin da ya hargitsa tare da haifar da rudani a bangaren.

  • Sin Ta Kulla Yarjejeniyar Tsarin Kafa Huldar Abota Ta Raya Tattalin Arziki Cikin Hadin Gwiwa Tsakaninta Da Kasashen Afirka 22.
  • Hukumar Zaɓe Ta Jihar Kano Ta Rage Farashin Takardar Tsayawa t Takara

Lamarin ya fi shafar masu masana’antu ne saboda karuwar farashi man fetur da karuwar farashi kayan da ake sarrafawa ya haifar da tsadar kayan aiki gaba daya.

Rahaoto ya nuna cewa, kudaden haraji daga bangaren masana’antu ya yi kasa da fiye da kashi 70 a zangon farko na shekarar 2024, wanda ke nuna irin matsalar da bangaren masana’antun ke fuskanta.

Haka kuma karyewar darajar naira ya sanya shigo da yayakin daga kasashen waje ya kara tsada, abin da ya kara hauhawar farashi da nakasa abin da yake hannun masu saye da sayarwa.

Wannan ya kuma rage bukatar da al’umma ke yi wa kayyakin da aka sarrafa a masana’antu, hakan ya kuma kara karya bangare gaba daya. Masu fashin baki sun bayyana cewa, wadanan tsare-tsaren tattalin arzikin, wanda zai hana masu masana’antu samun riba a harkokinsu.

Ana matukar sukar gwamnatin Nijeriya a kan yadda ta aiwatar da wadannan tsare- tsaren ba tare da cikakken tattaunawa tare da nema jin ra’ayin al’umma ba, ba kuma tare da ta samar da wasu hayoyin rage wa masu masana’antu radadin da za su shiga ba sakamakon wadannan tsare-tsare na gwamnati ba, haka ya sa ake ganin rashin kwarewar mukarraban gwamanatin da kuma kwarwarsu a bangaren farfado da tattalin arziki.

A tsokacinsa, shugaban kamfanin Coleman Wires and Cables Industries Limited, George Onafowokan, ya kwatanta shekarar 2024 a matsayin shekarar da ba ta yi wa masu masaa’antu dadi ba, ya bayar da misali karyewar darajar naira, jaye tallafin mai da kuma rashin tabbas a bangare tattali arzikin kasa a mastayin matsaloli da za su ci gaba da cutar da masana’atu a kasar nan.

A tattaunawar da aka yi da shi, ya ce, wadannan tsare-tsare sun yi matukar shafar bangaren masu masana’antu a sassan Nijeriya tun a watan Mayu na shekarar 2023, ya ce, zuwa yanzu ana ci gaba da karya darajar Naira, yayin da janye talafin mai ya haifar da karuwar kudin sufuri ya kuma shafi dukkan bangarorin tattalin arzikin kasa.

A cewarsa babu wani da bai dandana sakamakon matsalar tattalin arzikin nan ba domin shekarar gaba daya ta zo a hagunce ga dukkan bangarorin tattalin arziki Nijeriya musamman bangaren masana’antu.

“Ci gaban harkokin kasuwanci a yau na bukatar jajircewa mai yawa saboda rashin tabbas a bangarorin tattalin arziki da dama,” in ji Onafowokan, ya kuma ce, rashin tabbas a farashin naira ya sa ba zai yiwu mutum ya yi tsare-tsare da hasashen ko kuma tsara harkokin kaswuancinsa ba.

Ya kuma karfafa masu masaa’antua kan karfafa fata dukda mastralo,I da ake fuskanta, y ace, in har aka ki karfafa fata to daga karshe za a kai ga rufe masana’antun ke nan.

Onafowokan ya kuma ce, ya kamata gwamnati ta bayar da umarni samar da bashi ga ,masu masana’antu ta hanyar Bakin Masana’anatu, ya ce wanann mataki ne da zai farfado da masana’antu da dama a fadin kasar nan.

Ya kuma nemi a rage wa masu masaa’atu harajin da suke biya akan kayan da suke shigo da shi wadanda suke sarrafawa don tabbbatar da masana’antu na ci ga da rayuwa duk da matsalar tattali arzikj da ake fuskanta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma’adanai Don Kare Muhalli

Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma'adanai Don Kare Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version