Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Yadda Muka Kashe Yarinya, Muka Cire Al’aurarta Akan Naira 500,000

by Muhammad
January 11, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Yarinya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Rabiu Ali Indabawa,

An kama wasu mutane biyu da ake zargi da kisan wata yarinya a Bauchi, kuma sun a lokacin da aka kama su suke fada wa ’yan sanda dalilin da ya sa suka aikata wannan mummunar aikin. Wani shafin yanar gizo mai yada labarai, PRNigeria ya ruwaito cewa wadanda ake zargin, a cikin wani faifan sauti na tambayoyin sun furta cewa wani marabou Malamin duba ya ba su kwangilar kawo farjin karamar yarinya don yin tsafi kan kudi Naira 500, 000.

samndaads

Mutane biyun da ake zargi, Abdulkadir Wada, mai shekara 19, da Adamu Abdulrauf, mai shekara 20, sun yi ikirarin ne lokacin da jami’an rundunar ‘yan sanda ta Jihar Bauchi ke yi musu tambayoyi bayan an kama su. Da yake magana da harshen Hausa, Wada, babban mai laifin, ya ce shi da abokin aikin nasa, Abdulrauf, sun tafi Kwata, yankin da babban wansa yake wanda shi wan nasa yana aure.

Bayan sun isa yankin, sai suka kama wata karamar yarinya zuwa cikin wani gini da ba a kammala ba kuma suka shake ta har lahira. “Daga nan Abdulrauf ya zare wuka daga aljihunsa ya yanke al’aurar yarinyar. Marabout ne, wanda a yanzu haka ya gudu, ya nemi mu kawo masa wani bangare na jima’i a kan kudi Naira 500,000, ”in ji shi.

“Don haka, na tattauna da wani abokina wanda ake kira Musa wanda ya shawarce ni da in guji Wada. Washegari, yayin da nake shago ina aikin kanikanci, sai na hadu da Wada a gareji. Sannan ya bani wata (laya), wanda na jefa a cikin aljihu. Daga baya, mun sake haduwa da shi inda ya ce in raka shi zuwa wani wuri da ake kira Kwata.

“Lokacin da muka isa yankin, mun ga ‘yan mata biyu a wani wuri. Muka tsaya mun kira su. Wada yanzu ya cire wani kyalle daga aljihunsa ya haska shi a fuskar daya yarinyar, inda nan take yarinyar ta fadi, sai ya dauke ta zuwa cikin wani gini wanda ba’a kammala ba, kuma ya cire kayanta, kamar yadda Malamin dubar ya umurta. ”

A yayin haka kuma, Kakakin rundunar ‘yan sanda na Bauchi, DSP Ahmed Mohammed Wakil ya fada wa PRNigeria cewa nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan sun kammala bincike.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

’Yan Sanda Sun Tabbatar Da Satar Yara Bakwai A Zamfara

Next Post

Ya Yi Kokarin Yin Jima’i Da Gawa A Gaban ’Yan Uwanta

RelatedPosts

’Yan Sandan Italiya

’Yan Sandan Italiya Sun Kama ’Yan Nijeriya 16 Masu Sana’ar Miyagun Kwayoyi

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Rahotanni daga Kasar Italiya sun zo da ingacin cewa a...

miyagun kwayoyi

NDLEA Sun Cafke Mutum Uku Da Hodar Iblis A Legas

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA),...

’Yan Fashi

’Yan Sanda Sun Tabbatar Da Kisan Dan Uwan Akanta Janar Na ​​Imo

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

’Yan sanda sun tabbatar da kisan dan uwan ​Akanta Janar...

Next Post

Ya Yi Kokarin Yin Jima'i Da Gawa A Gaban ’Yan Uwanta

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version