Yadda Na Tsira Bayan Hukuncin Kisan Da Aka Yanke Min A Saudiyya -Adama Dadin Kowa
  • English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Tsira Bayan Hukuncin Kisan Da Aka Yanke Min A Saudiyya -Adama Dadin Kowa

byRabilu Sanusi Bena
2 years ago
Adama

Jarumar fina-finan Hausa ta Kannywood, Zuwaira Saleh Pantami wadda aka fi sani da Adama a cikin shiri mai dogon zango na Dadin Kowa, ta bayyana yadda aka yanke mata hukuncin kisa a Saudiyya.

Ta bayyana haka ne, yayin wata hira da jaruma Hadiza Gabon a cikin shirinta na Gabon’s Room Show.

  • Halittar Mata Na Canzawa Bayan Aure
  • Gwamna Uba Sani Ya Taya Sarkin Zazzau Murnar Cika Shekara Uku A Kan Karagar Mulki 

Ta bayyana yadda ta taka sawun barawo a kasar Saudiyya, har aka yanke mata hukuncin kisa.

Adama, ta bayyana cewa an taba yanke mata hukuncin kisa a kasar Saudiyya.

A cikin bayanin da ta yi tace sawun barawo ta taka Allah ne ya kubutar da ita, saboda ba ta aikata laifin da ake tuhumarta ba.

“Wani lokaci na je Umara, amma sai na tafi da irin tarkacen kayyayakin da ake tafiya da su daga nan Nalijeriya don na sayar a can,” in ji Zuwaira.

Ta ce na tafi da irin su daddawa, kuka, kubewa, goro da sauransu, “bayan na sayar sai na ga ribar da na samu har ta ninka jarin.

Sai kawai da na dawo Nijeriya sai na rika sarin irin wadannan kaya, ina tafiya da su Saudiyya, ina sayarwa, ina dawowa ina sake saye na koma.

“Na shafe lokaci mai tsawo ina yin haka, har sai ranar da aka kama ni wanda daga nan ne ban sake yi ba,” in ji ta.

Ta ce zuwan da ta yi na karshe wata rana tana cikin birnin Riyad, sai ta yi kacibus da wata kawa ta ‘yar asalin Sudan, sai ta nemi na rakata gida bayan na raka ta muna zaune a daki sai ga jami’an tsaro birjik.

Adama ta ce a nan aka tarkata dukkan matan da ke cikin dakin sai ofishin ‘yan sanda ,to a nan ne kawar tawa ta ce min gaskiya ke ba ki yi laifi ba, kin dai taka sawun barawo ne kawai.

Wannan kalami da jami’an tsaro su ka ji an yi a kai na ya yi sanadiyyar kubutata in ji Adama.

“Daga baya na gane ashe wai ana zargin sauran wadanda aka kama mu fa laifin kisan wani dattijo.”

Adama ta ce a karshe dai ita an sallame ta, amma sauran su bakwai duk an yanke masu hukuncin kisa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Next Post
Salon Shirya Hadadden Sandiwic

Salon Shirya Hadadden Sandiwic

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version