Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Yadda NULGE Neman Mamaye Gidajen ‘Yan Majalisar Dake Goyon Bayan Kudirin Cire Kananan Hukumomi

by
1 year ago
in MANYAN LABARAI
2 min read
NULGE
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Dga Rabiu Ali Indabawa,

Kungiyar Ma’aikatan Kananan Hukumomi ta Nijeriya (NULGE) na shirin gudanar da zanga-zanga domin mamaye gidajen kasar na dukkan ‘yan majalisar tarayya bisa nuna goyon baya ga kudirin da ke neman a soke majalisun kananan hukumomin da ‘yan majalisun suka yi.

Kungiyar ta ce duk masu goyon bayan kudirin makiyan Nijeriya ne da dimukradiyya, kuma ba su damu da halin kunci da bukatun shugabanci da ‘yan Nijeriya ke ciki a yankunan karkara ba. Shugaban NULGE Ambali Olatunji ya yi magana game da kudirin a gaban majalisar wakilai da ke neman soke matakin gwamnati na uku.

Labarai Masu Nasaba

Birtaniya Ta Kwato Dala Miliyan 23 Da Ake Zargin Marigayi Abacha Ya Sha Kwana Da Su

Barazanar Da Kilisar Matasa Ke Ci Gaba Da Yi A Kano

Wani dan majalisar wakilai, Bob Solomon, ne ke daukar nauyin dudurin dokar. Olatunji ya ce idan ba a kashe kudirin nan take ba, ma’aikata a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa za su gudanar da zanga-zanga a Majalisar Dokoki ta kasa, bayan haka za su mamaye gidajen kasar na dukkan mambobin majalisar.

“Ana barazana ga rayuwarmu; ba za mu zauna mu zuba ido muna kallo ba. Za a yi zanga-zangar kasa a can a Majalisa ta kasa. “Yanzu ba sa wakiltar mu, suna wakiltar kansu ne. Bob Emmanuel, wanda ya ci gajiyar tsarin kananan hukumomin, a yanzu ya zama abin takaici har yana son a soke tsarin.

“Shi dan jam’iyyar (PDP) ne shi ya sa muka nemi jam’iyya ta kira su domin su yi oda. Duk mutumin da ya yi yunkurin kashe tsarin kananan hukumomi yana kashe makomar siyasarsa ne. “Babu wani dan majalisar dokoki, wanda yake bangaren talakawa da ya kamata ya shiga wannan mummunar dabi’ar kuma ko waye sai mu yake su duka, ”in ji shi.

Shugaban na NULGE ya bukaci gwamnoni, wadanda suka yi imani da kananan hukumomi kuma suka gudanar da zabe a cikinsu, da su yi magana kan wannan shirin na dagula tsarin da ke kusantar da gwamnati kusa da mutane.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Ramadan:  Nasarorin Da Ake Samu A Watan Azumi Na Da Tasiri Da Gudummowr Mata – In Ji Dakta Zainab Bagudu

Next Post

Ministan Tsaro, Bashir Magashi Ya Ziyarci Maiduguri

Labarai Masu Nasaba

Birtaniya Ta Kwato Dala Miliyan 23 Da Ake Zargin Marigayi Abacha Ya Sha Kwana Da Su

Birtaniya Ta Kwato Dala Miliyan 23 Da Ake Zargin Marigayi Abacha Ya Sha Kwana Da Su

by Leadership Hausa
1 week ago
0

...

Kilisa

Barazanar Da Kilisar Matasa Ke Ci Gaba Da Yi A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 weeks ago
0

...

NSCDC

‘Yansanda Sun Lakada Wa Kwamadan NSCDC Na Jihar Imo Duka

by Khalid Idris Doya
2 weeks ago
0

...

Bana

A Shirye-shiryen Karamar Sallar Bana…

by Abdullahi Muh'd Sheka and Bello Hamza
2 weeks ago
0

...

Next Post
Ministan Tsaro, Bashir Magashi Ya Ziyarci Maiduguri

Ministan Tsaro, Bashir Magashi Ya Ziyarci Maiduguri

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: