Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Yadda Rikicin Boko Haram Ya Shafi Al’ummar Jihar Yobe

by Tayo Adelaja
October 4, 2017
in RAHOTANNI
3 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Sani Chinade, Damaturu

Al’ummar Jihar Yobe mutane ne waɗanda suka ɗanɗana kuɗarsu daga rikicin ‘ya ‘yan ƙungiyar Yusufiyya waɗanda aka fi sani da ‘yan ƙungiyar Boko Haram, na tsawon  shekaru 6, wanda a yanzu kusan za mu iya cewa lamarin ya zama tarihi kasancewar mafi yawan al’ummomin yankunan da suka yi gudun hijira sun koma garuruwansu na asali, musamman ma waɗanda  suka fito daga yankunan ƙananan Hukumomin Gujba da Gulani da a baya suke a hannun Boko Haram.

To amma duk da cewar wannan rikici na Boko Haram ya zama tarihi ga al’umma musamman ma garin Damaturu, fadar Jihar da abaya garin ya koma tamfar Kabul na kasar Afganistan, saboda tsananin yawaitar hare-hare masu zafi, da garin ya dinga fuskanta daga ‘yan Boko Haram. A halin da ake ciki al’ummomin wannan yanki na kokawa dangane abubuwan da suke addabarsu, sakamakon iftila’in da suka fuskanta a baya na rikicin Boko Haram, da suka haɗa da rashin aikin yi, tsadar rayuwa da kuma uwa ubansu rashin jari mai karfi daga ‘yan  ɓangaren kasuwa.

Kan haka ne wakilinmu ya samu tattaunawa da wasu al’ummar garin da suka tofa albarkacin baki kan waɗanda matsalolin da ke damunsu, inda suka ce saboda  rikicin Boko Haram ya kasance sanadiyar halin da suke ciki. Ga kaɗan daga ra’ayoyin al’umman yankin:

To Alhamdulilah a gaskiya kamar yadda ka ce rikicin  Boko Haram da mu ka yi fama da shi a wannan yanki na mu, na Yobe da ma wasu Jihohin maƙwabta irin su Jihar Borno da Adamawa da ya haifar mana da matsalar  taɓarɓarewar harkokin tsaro, lalle ya zama tarihi to amma kuma lamarin ya bar baya da ƙura saboda a halin da ake ciki yanzu mu al’ummomin wannan yanki musamman garin Damaturu garin da na ke mafi yawa-yawan  mu, muna fuskanta wasu matsaloli da in ba an kawo mana taimako ba, sai mu iya cewa har yanzu tsugunne bata ƙare ba.

Gaskiyar magana kaga dai lalle Allah cikin ikonsa ya raba mu da wannan rikici na Boko Haram da taimakonsa da kuma taimakon jami’an tsaron da suka jajirce a wannan karon  bugu da ƙari mun yi sa’ar samun shugaban ƙasa Muhammadu Buhari. To amma in ba an yi hoɓɓasan kawar da manyan matsalolin dake addabar mu da suka haɗa da rashin aikin yi, da tsadar rayuwa da kuna karancin jari ahannun ‘yan kasuwa ba to ai kaga akwai sauran lale. Babbar mafita ita ce dole na in gwamnati da gaske take to akwai bukatar samar da aiki ga matasa don rage shaye-shaye da sace-sace da kuma samar da abinci cikin sauki ga al’umma kana a kuma samar da jari ga ‘yan kasuwa ko da rance ne. To matukar anyi hakan za a samu sa’ida.

Oga Karumi (Shoe Shiner):

To sha’anin yanzu sai muce mun gode wa Allah amma  agaskiya a halin yanzu jama’a na cikin halin matsuwa.

Kamar yadda ka sani wato matsalar tsadar rayuwa kasancewar samun kuɗi al’amarin yayi ƙaranci, kuma farashin kayayyakin abinci ya wuce yadda kowa yake tsammani,  yadda  abubuwa na neman gagarar mai ƙaramin ƙarfi musamman ma talakka. Ka san shi dama ya saba da halin hannu baka hannu ƙwarya.

To a  gaskiya babban abin da nake sa rai akan  wannan lamari shi neroƙon Allah muke yi akan ya kawo mana ɗauki kamar yadda ya kawo, manataimakon  kawo ƙarshen rikicin Boko Haram,  su ma Hukumomi watogwamnatocin jiha jiha da ta Tarayya su gaggauta ɗaukar wani mataki da aka san zai kawo ma al’umma kwanciyar hankali.

Malam Musa Alhaji Adam:

Abin da nake nufi ai a baiyane yake ba a ɓoye ba domin a halin daake ciki hatta mu dake harkar Kasuwanci muna ji a jikin mu saboda kuwa harkar ciniki gaskiya, ba kamar yadda yake acan baya ba.

A ganina abin da ya haifar da wannan ai bai wuce halin matsin

rayuwa ba da muke fatan Allah cikin ikon shi ya kawo mana sauki yai mana taimako.

Abubakar Ɗan Ngamdu:

Al’amuran rayuwa a yanzu da a baya ai sai ayi shiru kawai.

Tun kawo ƙarshen  ta’addancin  Boko Haram a Yobe matsalar tsadar rayuwa ta

sako mu agaba a nan yanki, wadda mun san lamari ne daga Allah. Fatan mu

ya kawo mana ɗauki.

SendShareTweetShare
Previous Post

Dabara Ko Sakaci: Me Miƙa Tikitin Gwamna Ga Arewacin Jihar Nasarawa Ke Nufi?

Next Post

Za A Fara Sayar da Shinkafa ‘Yar Nijeriya A Farashi Naira Dubu Shida

RelatedPosts

Tuhumar Malam Abduljabbar Za A Yi, Ba Mukabala Da Shi Ba– Sheikh Khalil

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Nasir S. Gwangwazo, Abuja Shugaban Majalisar Malamai na Shiyyar...

ISWAP

Boko Haram Ta Yi Garkuwa Da Ma’aikatan Jinkai Bakwai A Dikwa

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri A harin bayan nan da mayakan...

Makanike

Shari’ar Gonaki: Kotu Ta Aike Wa Rundunar Soja Da Ma’aikarar Shari’a Sammaci

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Isa Abdullahi Gidan ‘Bakko, Zariya Kotun daukaka kara dake...

Next Post

Za A Fara Sayar da Shinkafa 'Yar Nijeriya A Farashi Naira Dubu Shida

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version