Yadda Sabon Irin ‘Tela Maize’ Zai Rage Asarar Da Manoman Masara Ke Yi
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sabon Irin ‘Tela Maize’ Zai Rage Asarar Da Manoman Masara Ke Yi

byAbubakar Abba
3 years ago
Tela Maize

Manoman Masara a Nijeriya suna gab da farfadowa daga irin asarar da suke tafkawa sakamakon barnar da kwari da kuma karancin ruwa da suke fuskanta a duk shekara, an kiyarsata asarar da ke yi ya kai na fiye da Naira Biliyan 9, wannan na faruwa ne sakamakon sabin irin masara na ‘Tela Maize’ da Cibiyar Binciken Harkokin Noma (IAR) da ke karkashin Jami’ar Ahmadu Bello Zariya ta samar ana kuma gab da fara gabatar dashi Manoman kasar nan.

A kasar da ke da mutane fiye da Miliyan 200 ana kuma samar da Tan Miliyan 12 na masara maimakon Tan Miliyan 18 na masara da ke bukata, a kan haka ake shigo da ragowa Tan miliyan 6 don cike gibin da ake bukata domin amfani a cikin gida.

  • 2023: Wasu Sun Yanki Fom Din Takara Na Miliyan 100 Don Fakewa Da Neman Minista —Okorocha

Baya ga dogaro da shigo da kayan abinci daga kasashen waje matsalolin sauyin yanayi ya sanya ana noma Tan 2.5 zuwa Tan 3 a hecta; tabbas wannan ya yi matukar karanci hakan kuma na daga cikin matsalolin da ke haifar da karancin abinci a wannan lokacin.

A jawabinsa a gonar gwaji na ‘TELA Maize’ da aka yi a karamar hukumar Minjibir ta Jihar Kano a makon jiya, Shugaban Cibiyar Binciken Aikin Noma (IAR) Zariya, Farfesa Mohammad Ishiyaku, ya bayyana cewa, an samar da sabon irin masara na ‘Tela Maize’ ta yadda zai iya jure farmakin kwari da kuma karancin ruwa, a halin yanzu manoma na tsimin fiye da Dala Biliyan 9 (Dala Miliyan 24) a duk shekara wajen magunguna kashe kari da suke saya don yin feshin kadadan fili noma da ya kai hekta 500.
Ya kuma kara da cewa, daga cikin Naira Biliyan 9 da aka kiyasta za a samu manoma za su yi tsimin Naira Biliyan 3 da ake kashewa wajen feshin kadada 500 za kuma a yi tsimin fiye da Naira Biliyan 6 na asarar da ke yi sakamakon illar rashin ruwa a duk shekara.
Farfesa Ishiyaku ya bayyana cewa, IAR ta samu gaggaruwa nasara a fannoni da fama tun da aka fara binciken samar da irin ‘TELA Maize’ musamman a kan gonakin gwaji da aka kafa a sassan kasar inda aka fahimci yadda irin ke iya jure wa fari da farmakin kwari. Ya ce, wadannan nasarorin za su taimaka wajen warware matsalolin da manoma ke fuskanta tare da bunkasa tattalin arzikin kasa wanda zai kai Nijeriya ga dogaro da kai a wajen samar da abinci ga ‘yan kasa.
Ya kuma bayyana cewa, a tsawon shekara 100 da kafa Cibiyar Binciken Harkokin Noma (IAR) na Samaru ta gudabar da bincike da dama a kan kayyakin noma daban-daban wadanda suka kai ga kara yabanyar da manoma ke samu da kuma bunkasa tattalin arzikinsu gaba daya.
A nashi jawabin, shugaban kwamitin samar da irin ‘TELA Maize’ a Nijeriya, Farfesa Rabiu Adamu, ya ce,an fara bincike don samar da irin a Nijeriya ne tun a shekarar 2019 an kuma yi haka ne saboda matsalolin da kwarin ‘Fall armyworm’ da ‘Stem-borers’ ke haifarwa a kan masara wanda hakan ke janyo asarar fiye kashi 80 na masarar da ake nomawa a fadin kasar nan.
Farfesa Rabiu Adamu wanda masani ne a bangaren kwari da yadda suke barnata shuka, ‘Entomology’, ya ce, samar da irin ‘TELA Maize’, zai taimaka wajen rage yadda manoma ke amfani da magunguna kashe kwari wanda hakan zai takaita yadda amfanin dasu ke cutar da muhalli da rayuwar al’umma. Ya ce, samar da ‘Tela Maize aiki ne na wata hadaka data hada da Gidauniyar Inganta Aikin Gona ta Afrika (AATF) a kasasshen Afrika 7 wanda suka hada da Kenya, Uganda, Tanzania, Ethiopia, Mozambikue, Nijeriya da kuma Afrika ta Kudu.
Manoman sun yi maraba tare da nuna jin dadinsu a kan samar da ‘Tela Maize’ wanda suka ce, tabbass zai bunkasa harkar noma a Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Bishiyar Dogon-yaro

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Bishiyar Dogon-yaro

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version