Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja

byAbubakar Abba
1 year ago
Wike

Ayyukan ci gaba da aka samar a cikin shekara daya a Abuja, babban birin tarayya, a karkashin shugabancin ministan, Nyesom Wike hakan ya yi matukar janyo hankalin Shugaban kasa, Bola Tinubu da kuma mazauna birnin wajen jinjina wa Wike.

Babu wata tantama, tauraruwar Wike ta haska a idon gwamnatin Tinubu a cikin shekara daya da ta gabata.

  • Xi Ya Yi Rangadi A Lardin Qinghai Da Jihar Ningxia
  • Kotu Ta Rushe Dokar Da Ta Tsige Aminu Ado Bayero A Matsayin Sarkin Kano

Bisa wannan ayyukan na ci gaba da Wike ya samar a Abuja, za a iya cewa tamkar ya dora ne kan irin ayyuakn ci gaba da ya samar a lokacin da yake kan karagar mulkin Jihar Ribas, inda ya yi wa’adin mulkinsa na tsawon shekaru takwas wanda har aka yi masa lakabi da sarkin aiki.

A nan za a iya cewa, nada Wike da Tinubu ya yi a matsayin ministan ya sanya shi farin ciki saboda ayyukan ci gaba da ya samar a Abuja, wanda da a ce, Tinubu ya biye wa surutun mutane na kiraye-kirayen da sukai ta faman yi na ganin cewa ba a nada Wike a mukamin minista, da yanzu irin wannnan ayyukan na ci gaba ba za a samu a Abuja ba.

Shi kan shi Tinubu ya tabbatar da cewa, wasu suka ba shi shawara kar ya nada Wike a wani mukami a cikin gwamnatinsa.

Tinubu ya tabbatar da hakan ne a lokacin kammadar da aikin titin ‘Arterial’ da ke a cikin Abuja wadda aka kashe naira miliyan 20, kuma sauya sunan titin zuwa Wole Soyinka Way.

Tinubu ya ce, “Mai girma minista na zo wajen kaddamar da aikin ne domin na gode maka kai da tawagarka, musamman bisa samar da cin nasara ga gwamnatinmu a cikin shekara daya. Ayyukan da ka gudanar a birnin Abuja sun sa mutane sun ji dadi sosai.

“Zuciyarta na cike da farin ciki da kuma alfahari da kai, domin sun yi tunanin cewa Wike ba zai iya yin wani aikin a zo a gani a matsayin minista ba, sai kuma gashi ba ka bai wa mara da kunya ba. Ayyuakan da kake kirkiro da su a birnin Abuja abun yaba wa ne.

Wike daga jam’iyyar PDP ya fito, wanda kuma ya karbi ajandar shirin Tinubu na magance kalubalen tattalin arziki, rashin tsaro da kuma samar da aikin yi tun lokacin kaddamar da yakin neman zaben 2023, da ake kira a turance, ‘Renewed Hope Agenda’.

Bugu da kari, bisa ayyukan ci gaba da Wike ya kirkiro da su a birnin a cikin shekara daya, wadanda kuma ana ganin su a zahari, hakan ya sanya an samar da sauye-sauyin na ci gaba a birnin a fannoni da dama.

Kazalika, a tarihin birnin ba a taba shafe kwanuka tara cur ana kaddamar da wasu ayyuka da aka yi a birinin ba, sai a lokacin mulkin gwamnatin Tinubu, inda shugaban ya kaddamar da ayyuka daban-daban da aka kirkiro da su a karkashin jagorancin Wike.

Ayyuakann sun hada da, kara kaddamar da aikin safarar jirgin kasa da zai yi zirga-zirga a cikin garin Abuja mai daukar fasinjoji kyauta har tsawon watanni bakwai da aikin gina titin ‘Southern Parkway, S8/S9; da na Christian Centre zuwa titin Ring Road 1; da titin B6, B12, da na Circle da aikin gadar Wuye da gidan mataimakin shugaban kasa da suka lashe kudi har naira biliyan 98.8.

A cewar Wike, kaddamar da wadannan ayyukan, sun nuna a zahairi gwamnatin Tinubu ta mayar da hankali wajen inganta harkokin kasuwanci da kuma inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

A lokacin sake kaddamar da aikin jirgin kasan, Wike ya ayyana yin jigilar matafiya kyauta har na tsawon wata biyu, wanda saboda jin dadin wannan ayyanawar ta Wike, sai Tinubu ya kara fadada jigikar zuwa watan Disamba domin a nuna jin kan gwamnatinsa take da shi ga ‘yan Nijeriya a fannin zirga-zirga.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, hukumar kula da raya birnin Abuja ce ta bayar da kwangilar aikin zirga-zirgar jiragen kasa a cikin birnin a 2007, inda aka fara gudanar da aikin gwaji na aikin daga watan Satumban 2018, inda aka kammala aikin a watan Maris na 2020.

Sai dai aikin zirga-zirgar jirgin ya samu koma baya sakamakon bullar annobar Korona da sace wasu manyan kayan aikin wanda hakan ya janyo aikin ya tsaya cak tun a 2020.

A yayin kaddamar da ayyukan titunan Southern Parkway, S8/S9 da na Christian Centre zuwa titin Ring 1, Tinubu ya ce, kammala ayyukan sun nuna zahirin manufar gwamnatinsa da gaske take don samar da ayyukan ci gaba.

Tinubu ya kaddamar da ayyukan da aka kashe naira biliyan 98.8 na aikin hanyoyin B6, B12 da na Circle da ke birnin, ya ce za su kara bunkasa kasuwanci da kuma inganta raruwar ‘yan Nijeriya.

A cewar Tinubu, zai iya bugun kirji da cewa ya kaddamar da ayyukan hanyoyi B6, B12 da na Circle a tsakiyar birnin Abuja a karkashin kulawar Wike. Ya ce wannan ayyukan tamkar zakaran gwajin dafi ne ga mulkinsa.

Aikin gadar Wuye da za ta sada sauran gundumomin da birnin na daga cikin manyan ayyukan ci gaba da Wike ya samar, domin sama da shekaru 20 da suka gabata ba a yi hakan ba.

Tinubu ya jinjina wa Wike bisa sadaukar da kai na cimma muradun ajandar shugabancinsa da ake kira a turance, ‘ Renewed Hope Agenda’, musamman bisa yadda a zahiri ajandar ta inganta rayuwar mazauna birnin.

A makon da ya gabata ne, aka kammala kaddamar ayyukan a cikin kwana tara, inda Tinubu ya sauya wa babban titin M18 da ke a yankin Guzape Lot II a Abuja, zuwa sunan Chinua Achebe.

Wike ya yi alkawarin kammala ayyukan da ke a yankin jakadu da ke a birnin tare da kuma bai wa Tinubu tabbacin kammala ayyukan a shekara mai zuwa.

Tun a farko, Wike ya kaddamar da ayyukan manyan hanyoyi tare da giggina makarantu a yankuna shida na birnin wadanda idan an kammala su, za a kaddamar da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya amsa Tambayoyin ’Yan Jaridu Game Da Sayarwa Taiwan Makamai Da Amurka Ta Yi A Sabon Zagaye

Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya amsa Tambayoyin ’Yan Jaridu Game Da Sayarwa Taiwan Makamai Da Amurka Ta Yi A Sabon Zagaye

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version