Yadda 'Yar Hidimar Kasa Ta Gwangwaje Guragu Da Kekunan Hawa 100 A Bauchi
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yar Hidimar Kasa Ta Gwangwaje Guragu Da Kekunan Hawa 100 A Bauchi

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Wata mai yi wa kasa hidima (NYSC) wacce take aikin hidimar kasa a karamar hukumar Gamawa da ke jihar Bauchi, Khadija Lukman ta gwangwaje mutane masu fama da lalura ta musamman a karamar hukumar da Kekunan Hawa guda 100 domin saukaka musu gudanar da harkokin rayuwa. 

Khadija mai lambar shaidar hidimar kasa BA/23A/3158 ta bayyana a wajen bikin mika kekunan hawan a ranar Juma’a cewa, wannan wani mataki ne na cika alkawarin da ta yi na cewa za ta taimaka wa masu fama da bukata ta musamman tun lokacin da take makaranta.

  • Jihar Kaduna Ta Fara Ƙwaƙƙwaran Bincike Kan Yadda Lassa Ta Kashe Mutane A Asibitin Sojoji
  • Yadda Zaki Ya Halaka Mai Ba Shi Abinci Har Lahira

A cewar jarumar matashiyar, wannan tallafin nata ta bayar ne ba wai domin ta karfafa wa wadanda suka ci gajiyar kekunan cigaba da yin barace-barace ba, illa domin ta taimakesu da karfafa musu guiwa wajen zirga-zirgan neman inganta rayuwarsu.

Khadija ta jawo hankalin wadanda suka ci gajiyar da kar su yi kasa a guiwa ko cire tsammani wajen fafutukar cika burikan rayuwarsu a kowani lokaci.

Khadija ta ce ta samu tallafi wajen aiwatar da wannan kyakkyawar aikin nata ne da gudunmawar daraktan cibiyar Beautiful Gate Handicap da ke Jos ta jihar Filato, Barista Ayuba Gufwan.

A gefe guda, mambar hukumar kula da matasa masu yi wa kasa hidima, ta kuma horas da matasa sama da 100 kan yadda za su hada sabulu, man shafawa, kamshin daki da dai sauransu.

Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar, Fatima Muhammad, ta gode wa ‘yar Hidimar kasar da wanda ya dauki nauyin tallafin bisa taimaka musu, ta musu addu’ar Allah saka musu da alkairi.

A bangarenta, ko’odinetar hukumar kula da matasa masu yi wa kasa hidima (NYSC) a jihar Bauchi, Rifkatu Yakubu, ta jinjina wa matashiyar ne bisa gudanar aikin da kai tsaye zai kawo sauki ga mutane masu fama da bukata ta musamman.

Kan hakan ne ta yi kira ga masu hannu da shuni da gwamnatoci da su karfafawa matasa masu yi wa kasa hidima da ke da kyakkyawar niyya da tsarin da za su taimakawa al’umma a kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

Rikita-rikitan Barazanar Yanke Wutar Fadar Shugaban Kasa: Tinubu Ya Ba Da Umurnin Biyan Kudin

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version