Yadda Zargin Horo Da Ruwan Zafi Ya Jefa Rayuwar Budurwa Cikin Larura
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Zargin Horo Da Ruwan Zafi Ya Jefa Rayuwar Budurwa Cikin Larura

byRabi'u Ali Indabawa
12 months ago
Horo

‘Yan uwan wata budurwa ‘yar shekara 23 mai suna Nana Fiddausi Sa’idu da ke da zama a Unguwar Makera gudunmar Rigasa a Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna, sun yi kira ga masu hannu da shuni, da su taimaka wa rayuwar buduwar, biyo bayan kamuwa da wata larura wanda hakan ya janyo halitta ta koma tamkar, ta karamar yarinya.

Wata kanwar mahaifiyarta mai suna A’i ta yi zargin cewa, Nana ta kamu da larurar ce, bayan da mahaifin Nana ya dauke ta daga gun dangin mahaifiyar ta ya kuma ya mayar da ita ga wata ‘yaruwarsa da ke a Jihar Kano.

  • Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
  • Ronaldo Da Messi Ne Kan Gaba A Jerin ‘Yan Wasan Da Suka Fi Karbar Albashi

Ta ce, lafiyar ta lau mahaifinta ya dauke ta daga wurinsu amma sai ta gudo daga gun ‘yaruwar ta sa daga Kano saboda ‘yar uwar uban, na yi mata mata horo da ruwan zafi.

A cewarta, Nana ta je tashar mota ta Kano ne, inda ta nemi taimakon mutane da su sanya a mota ta dawo Kadauna, suka dauko ta suka kawo ta gidanmu.

Ta ce, bayan da Nana ta kamu da larurar babu wata kulawa daga mahaifinta, ya yi wasti da ita, kuma ‘yanu wansa babu wanda ya damu da halin da take a ciki.

Ta ce, bayan kwana biyu ta fadi aka kaita asibitin Nasiha ba a cikin hayyacinta ba, aka kwantar da ita, a rika kiran mahaifinta a waya, daga baya ya zo ya iske, ana yi mata karin ruwa, sai ya cire robar karin ruwan har suka fara sa-insa da wata jami’ar asibitin, amma ya matsa sai da aka cire mata aka dawo da ita gida.

Ai ta ce, larurar ta koma mata kamar farfadiya, wanda duk inda take, sai ta fadi tana fisge-fisge, yanzu gashi mahaifinta ya rasu, kuma ‘yanuwansa, babu wanda ya damu da halin laruwar da take ciki.

Da aka tambaye ta ko sun sanar da hukuma lamarin ta ce, ba a sanar da hukuma ba, inda ta ce, tun ana yi mata magani, yanzu dai karfinsu ya kare, amma suna neman taimako don a ceto raywarta.

Shi ma Ibrahim Hannafi wanda yayan mahaifiyar Nana ne, ya zargi ‘yan uwan mahaifi da nuna halin ko in kula a kan larurar Nana, inda ya yi kira ga masu hali, da su taimaka a ceto raywar budurwar.

Ya ce, lokacin mahaifinsu yana raye, shi ne yake kulawa da halin da take ciki amma ya ce, mu kyale, ‘yan uwan mahaifinta da halin sun nuna ko in kula dangane da larurar ta, kuma bai bar su mun dauki wani mataki ba a lokacin da yake raye.

Shi kuwa Malam Anas Musa dan kungiyar kare hakkin ‘yan’Adam cewa ya yi, an zalunci yarinyar, duba da yadda dangin mahaifinta suka yi watsi da ita, suka bar nauyinta a gun dangin uwarta, inda ya ce, a kungiyance, za mu bi wa Nana kadin tauye mata ‘yancinta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohowar Shugaban Kotun Gargajiya A Benue

Kotu Ta Garkame Wani Dan Shekara 43 Da Ya Lalata Agolarsa

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version