Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Yaduwar Korona: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tilasta Sanya Takunkumin Baki

by
2 years ago
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Yaduwar Korona: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tilasta Sanya Takunkumin Baki
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Gwamnatin tarayya tana duba yiwuwar tilasta wa al’ummar kasar nan sanya hular nan ta toshe baki da hanci domin dakile yaduwar annobar Koronabairus inda ko ajiya, sai da masu dauke da cutar suka karu da mutane Takwas wanda a yanzun adadin masu dauke da cutar a kasar nan ya kai 139.

Domin kuma kara himma kan kula da wadanda suka kamu da cutar, gwamnatin ta kirayi jami’an lafiyan da suka yi ritaya, wadanda a yanzun haka ake ba su horo a kan yanda za su tallafi bayar da magani ga masu dauke da cutar.

Sauran matakan da gwamnatin ke dauka domin dakile yaduwar cutar sun hada da samar da karin cibiyoyin yin gwaji ta yanda Nijeriya za ta iya gwada akalla mutane 1500 a kowace rana domin hanzarta gano masu dauke da cutar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

Kididdiga daga cibiyar kula da cutuka ta kasa (NCDC), ta nuna cewa a yanzun haka kasar nan ta yi gwajin kamuwa da cutar a kan mutanan kasar nan guda 2,000 tun daga lokacin da aka shelanta barkewar cutar a kasar nan a ranar 27 ga watan Fabrairu, 2020.

Hakanan, gwamnatin tarayya tana duba yiwuwar samar da dan wani tallafi domin amfanar mutane milyan 11 da suke fama da kunci a sakamakon barkewar cutar ta Koronabairus.

Da yake magana jiya a wajen taron manema labarai, shugaban hukumar ta NCDC, a kan yaki da annobar ta Koronabairus, Dakta Chikwe Ihekweazu, cewa ya yi hukumar na su tana duba yiwuwar tilasta wa al’ummar kasar nan sanya hular ta toshe baki da hanci domin dakile yaduwar cutar ta Koronabairus.

Ihekweazu ya yi nuni da cewa, hukumar lafiya ta Duniya (WHO), ta bayar da shawarar cewa ma’aikatan sashen lafiya ne kadai za su rika sanya hular ta toshe baki da hanci domin kare kansu daga kamuwa da cutar.

Ya ce, tabbas cibiyar na su tana duba yiwuwar hakan a bisa sabbin dalilan da suke ta bayyana, ya kara da cewa, domin tabbatar da aikin hular ta rufe baki da hanci ga al’ummar kasa, cibiyar na su za ta bayar da shawarar kowane dan kasa ya rika yin amfani da ita.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

ASUU Za Ta Tallafa Wajen Yaki Da Korona

Next Post

Yakamata Masu Karfi Su Tallafi Marasa Karfi A Wannan Yanayin – Dankaden Zazzau

Labarai Masu Nasaba

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by
1 year ago
0

...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by
1 year ago
0

...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by
1 year ago
0

...

Kebbi

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by
1 year ago
0

...

Next Post
Yakamata Masu Karfi Su Tallafi Marasa Karfi A Wannan Yanayin – Dankaden Zazzau

Yakamata Masu Karfi Su Tallafi Marasa Karfi A Wannan Yanayin – Dankaden Zazzau

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: