Yajin Aikin ASUU: Ba Za Mu Sarara Ba Har Sai Gwamnati Ta Magance – NLC
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: Ba Za Mu Sarara Ba Har Sai Gwamnati Ta Magance – NLC

byYusuf Shuaibu
3 years ago
NLC

Kungiyar Kwadago ta Kasa(NLC) da sauran dukkan gwamayyar kungiyoyi da suka gudanar da zanga-zangar lumana ta kwanaki biyu a fadin kasar nan, sun bayyana cewa ba za su sarara ba har sai gwamnatin tarayya ta kawo karshen yajin aikin Kungiyar Malaman Jami’o’in Nijeriya (ASUU).

Sun bayyana cewa manufar wannan zanga-zangar dai ita ce, tilasta wa gwamnatin tarayya ta biya bukatun ASUU, domin a bude jami’o’in gwamnatin taraya ta yadda dalibai za su ci gaba da daukan darasi.

Yadda ’Yan Kasuwa Suka Rufe Kasuwanni A Legas Don Yankar Katin Zabe

Da yake jawabi ga ma’aikata a Abuja, shugaban kungiyar NLC na kasa, Kwamared Ayuba Wabba ya jaddada cewa, kungiyar ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai gwamnatin tarayya ta biya dukkan bukatun kungiyar ASUU.

Kwamared Wabba ya bayyana cewa babu wani dalilin da zai sa yaran talakawa za su ci gaba da zama a gidan iyayensu na tsawan watani biyar, yayin da ‘ya’yan masu kudi suke ci gaba da karatu a kasashen ketare.
Ya ce, “Babu adalci a cikin wannan lamari idan har gwamnati ta kasa kawo karshen lamari, ba za mu taba gajiya ba kuma ba za mu yi fushi ba, saboda ba wannan yarjejeniya muka kulla da shugabannin da muka zaba ba.

“Wannan somin-tabi ne, dole ne ku yi shirin fargfado da bangaren ilimi, mun gaji da halin ko-in-kula na gwamnati, dole ne mu rungumi kaddara a hannunmu.
“Sun ce muna janyo barazanar tsaro, amma abin da su suke yi baraza ce da dimokuradiyya, za mu sake saita kasar nan ta yadda shugabanninmu za su gudanar da abubuwan da suka dace.

“Muna yaba wa gwamnoni wadanda suka fito domin yin jawabi, muna bukatar gudanar da tattauna ta yadda za a kawo karshen lamarin, ba za mu taba yarda mutane kalilan su ruguza goben yaran Nijeriya ba,” in ji shi.
Shi ma da yake gabatar da jawabi, shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya bayyana cewa dole ne gwamnatin tayya ta kaddamar da tsarin gudanarwa na biyan malaman jami’o’i.

Hakazalika, kungiyar NLC reshan Jihar Legas ta bai wa gwamnatin tarayya wa’adin makanni biyu na kawo karshen yajin aikin ASUU ko kuma ta fuskanci zazzafar zanga-zanga.

Shugaban kungiyar NLC reshan Jihar Legas, Kwamared Agnes Funmi Sessi shi ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi a gaban dinbin masu zanga-zanga a ofishin gwamnatin Jihar Legas. Ya nuna takaicinsa ta yadda iyaye da dalibain jami’o’in gwamnatin tarayya suke ciki, inda ya ce shi ne makasudin gudanar da wannan zanga-zanga na gargadi.

A ranar 26 ga watan Yulin 2022, kungiyar NLC ta gudanar da zanga-zangar gargadi na kwanaki biyu a dukkan fadin kasar nan, sakamakon gwamnatin tarayya ta kasa kawo karshen yajin aikin kungiyar ASUU. Kungiyar ta gargadin gwamnatin tarayya kar ta dauki wannan zanga-zanga da wasa, domin idan har ta yi kunnen kashi, to zanga-zangan za ta iya rikidewa fiye da wanda aka samu na EndSARS a shekarar 2020.

Kungiyar ASUU ta tsunduma cikin yajin aiki na tsawan watanni biyar, sakamakon rashin cika mata alkawarin da gwamnatin tarayya ba ta yi ba, wadanda suka hada da alawus din malaman jami’o’i da gyara tsarin jami’o’in Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Kwamitin Binciken Tallafin Mai Na Tsare-tsaren Neman Mafita – Hon. Almustapha

Kwamitin Binciken Tallafin Mai Na Tsare-tsaren Neman Mafita - Hon. Almustapha

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version