'Yan Adawa Ku Zo Mu Yi Aiki Tare A Katsina - Mai Ba Gwamna Shawara
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Ku Zo Mu Yi Aiki Tare A Katsina – Mai Ba Gwamna Shawara

byEl-Zaharadeen Umar
2 years ago
Katsina

Mai ba gwamnan jihar Katsina shawara kan harkokin siyasa, Hon. Yau Umar Gwajo-Gwajo, ya yi kira ga ‘yan adawa da su zo a yi gwamnati domin ci gaban al’ummar jihar Katsina baki ɗaya.

Hon. Ya’u Gwajo-Gwajo ya yi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai jin kaɗan bayan shigarsa sabon ofis na mai baiwa gwamna shawara kan harkokin siyasa.

Tsohon Kakakin Majalisar dokokin ya ce, in dai da gaske adawa ake yi, to yana kira da babbar murya da su zo a haɗa kai a ciyar da jihar gaba domin duk abinda ake yi ana yi ne domin talaka.

Hon. Gwajo-Gwajo ya ce a shirye suke da sauraren suka mai ma’ana, domin a cewarsa suka ba laifi ba ne, idan har zata sa abyi gyara wanda zai amfani al’umma baƙi ɗaya.

“Muna son ɗan adawa ya zo ya faɗi abinda yake ganin ba daidai bane, muna san haka, domin shi duk wanda ya ce gyara kayanka ai baya zama sauke mu raba” Cewarsai.

A cewar Hon. Yau Umar Gwajo-Gwajo abinda ba daidai ba shi ne, a kawo abu da babu shi, amma don gwamnati ta ce zata yi wani abu ɗan adawa ya ce ba daidai bane, za a tsaya a duba wannan abu a gani domin samun maslaha.

‘Yan adawa muna maraba da ku, muna gayyatar ku, ku zo a yi wannan gwamnati da ku, domin ta haka ne jihar Katsina zata kai wani matsayi da ba a tunani’ inji Gwajo-Gwajo.

Haka kuma ya yi kira ga ‘yan jarida da su bada ta su gudunmawa wajan ganin wannan gwamnati ta Malam Dikko Raɗɗa ta yi nasara, inda ya ce ‘yan jarida suna muhimmiyar rawar da za su taka wajan kawo gyara a tsarin dimokuraɗiyya.

Ya yi kira ga ‘Yan jarida da su ci gaba da aikinsu ta hanyar tuntuɓar gwamnati akan abinda ya shafe ta kai tsaye, inda ya yi alkawarin cewa kofa a buɗe take akan duk wani ƙarin haske daga ɓangaren gwamnati.

Kazalika ya bada tabbacin cewa wannan ofis ɗin shi, a shirye yake wajan ganin ya yi aiki da kowane ɓangare tunda ofis ne na siyasa, a cewarsa ofis ɗin yana da alaƙa da kowane ɓangare na gwamnatin jihar Katsina.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Next Post
Ministar Ghana Ta Yi Murabus Bayan Sace Makudaden Kudade A Gidanta

Ministar Ghana Ta Yi Murabus Bayan Sace Makudaden Kudade A Gidanta

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version