‘Yan Bindiga Na Sake Hada Gungu Duk Da Farmakin Sojoji
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Na Sake Hada Gungu Duk Da Farmakin Sojoji

byRabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Sojoji

Duk da hare-hare gami da fatattakar da sojoji ke yi wa ‘yan bindiga, ga dukkan alamu ‘yan bindigar dake yankin Arewa maso yammacin Nijeriya na ci gaba da hadewa suna kai hare-hare a Maradun da Zuru, a Zamfara da kuma Karamar Hukumar Kankara a Katsina cikin kwanaki 3 da suka gabata.

LEADERSHIP Weekend ta ruwaito daga majiya mai tushe ta rundunar ‘yansandan Jihar Zamfara cewa kwanaki ukun da suka gabata an fuskanci matsi sakamakon hare-haren da ‘yan bindiga ke kaiwa.

  • Matsalar Ruwan Sha: Yara 9 Sun Mutu A Kwale-Kwale, 12 Sun Bace A Zamfara
  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Sake Kutsawa Garin Abuja, Sun Sace Mutane 4

‘Yan bindiga sun kuma kai hari tare da kashe sojoji 6, biyu daga cikinsu jami’ai ne a karamar hukumar Shiroror ta jihar Neja, jihar ta Arewa ta tsakiya wacce ke kan iyaka da Kaduna da Kebbi, dukkansu jihohin Arewa maso Yamma.

Sojojin Nijeriya tare da hadin gwiwar jami’an tsaron farin kaya (DSS) sun dakile harin ‘yan ta’adda a Jihar Sokoto, inda suka kashe bakwai daga cikin ‘yan ta’addan.

A wata sanarwa da rundunar sojin Nijeriya ta fitar akan shafinta na D ta ce dakarun da ke jiran ko-ta-kwana sun kama wasu ‘yan ta’adda dauke da makamai a wani farmaki da suka kai a yankin Modachi na Karamar Hukumar Isa ta Jihar Sakkwato.

Sanarwar ta ce dakarun da ke aikin hadin gwiwa sun kashe 7 daga cikin ‘yan ta’adda tare da kwato manyan tarin makamai.

‘Yan ta’adda da ke wucewa da babura da dama, jami’an tsaro sun yi artabu da su, lamarin da ya kai ga halaka ‘yan ta’adda bakwai.

Sannan Sojojin sun kwato bindigogi kirar AK-47 bakwai, babura hudu, wayoyin hannu biyu, da adduna hudu.

Sojojin Nijeriya a cikin makonni uku da suka gabata sun kashe ‘yan ta’adda 31 a yankin Arewa maso Yamma, gami da kwato wasu makamai tare da rasa sojoji 7 a wani harin kwantan bauna.

A harin na baya-bayan nan, an bayyana cewa wasu ‘yan bindiga a Katsina sun kashe wani jami’in runduna ta 17 na sojojin Nijeriya, Manjo A.G Mohammed.

Marigayi Mohammed mamba ne na Operation Hadarin Daji kuma kwamandan da ke kula da ayyukan soji a Bantumaki, Dan Ali da Kankara a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Kyawawan ‘Yan Mata Da Suke Shiga Harkar Fim Suna Bata Rayuwarsu -Kyauta Dillaliya

Kyawawan 'Yan Mata Da Suke Shiga Harkar Fim Suna Bata Rayuwarsu -Kyauta Dillaliya

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version