Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

’Yan Bindiga Sun Hallaka Jami’an NDLEA A Kogi

by Tayo Adelaja
October 16, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Idris Aliyu Daudawa

Hukumar hana sha da kuma safarar miyagun ƙayoyi ta ƙasa NDLEA ta yi asarar jami’anta uku, waɗanda ‘yan bindiga daɗi suka hallaka a Okene jihar Kogi.

samndaads

Kwamandan Hukumar mai kula da jihar Kogi Idris Bello ya faɗawa manema labarai ranar Lahadi, an kasha mutanen uku ne lokacin da suke cikin aikinsu.

Ya ce, an hallaka su ne misalin ƙarfe uku da rabi, 8:30 ranar 13 ga Oktoba, ‘yan bindigar sun yi shigar burtu ne lokacin da suka kawo samamen.

Jami’an uku da suka rasa rayukansu sun haɗa da Nicholas Onwumere, Ebun Peters, da kuma Abdulrahman Musa.

Kwamandan ya ce su jami’an NDLEA suna cikin aikin su da sauran abokan aikin nasu uku ne, yan bindigar suka kawo harin. Jami’an uku sun mutu nan take ne, su kuma abokan aikin nasu sun yi sa a ba bu ko ƙwarzane a jikinsu. ‘Yan bindigar sun yi awan gaba da bindigogin ‘jami’an uku da suka kashe.

Ya ƙara jaddada cewar an sanar da sauran ‘jami’an tsaro da ke jihar, a halin da ake ciki, ana kuma yin duk koƙarin da yakamata wajen kama ‘yanbindigar.

Gamantin jihar Kogi watan Agusta ne ta kafa wata rundunar  tsaro mai suna Forward Operation Base a Okkene tare da haɗin kai da Rundunar Soja ta ƙasa, saboda a samu dama ta yin wani abu dangane da garkuwa da Jama’a, fashi da makami, da kuma sauran ayyukan ashsha. Wannan ƙoƙarin da aka yi dai har yanzu bai haifi ɗa mai ido ba, kamar yadda masu lura da al’amura suka ce.

Suna ganin wannan harin ma watakila ƙungiyar Boko Haram ce, wadda ta riƙa cin karenta babu babbaka a Arewacin Najeriya.Bayan da Rundunar Sojoji ta ƙasa ta karairaye masu laka.

SendShareTweetShare
Previous Post

Akwai Buƙatar A Farfaɗo Da Mutuncin Kaduna -Alhaji Uba Lamuni

Next Post

Ƙaramar Hukumar Gaidam Za Ta Horas Da Matasa 100 Sana’o’i

RelatedPosts

Masana Sun Yaba Wa Shugaba Buhari Kan Sake Nada Hadiza Bala Usman Shugabar NPA

Masana Sun Yaba Wa Shugaba Buhari Kan Sake Nada Hadiza Bala Usman Shugabar NPA

by Sulaiman Ibrahim
7 mins ago
0

Daga Bello Hamza, Abuja Masana da masu ruwa da tsaki...

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

by Muhammad
1 hour ago
0

Rahotanni daga jihar Zamfara sun tabbatar da cewa an ceto...

IITA Ta Fara Horas Da Matasa Sana`o`in Dogaro Da Kai A Zariya

IITA Ta Fara Horas Da Matasa Sana`o`in Dogaro Da Kai A Zariya

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Nasiru Adamu Cibiyar kula da albarkatun aikin gona ta...

Next Post

Ƙaramar Hukumar Gaidam Za Ta Horas Da Matasa 100 Sana’o’i

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version