Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

‘Yan Bindiga Sun Harbe Dan Sanda A Bauchi

by Muhammad
March 14, 2021
in LABARAI
1 min read
Kogi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya,

Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba, sun yi kwantan bauna inda suke farmaki ‘yan sanda da ke suntiri a kauyen Nabordo da ke cikin garin Bauchi inda suka hallaka wani dan sanda mai mukamin Insifekta Mukhtar Ibrahim dan shekara 35 a duniya.

Da ya ke tabbar da faruwar lamarin a cikin sanarwar da ya aiko mana, Kakakin ‘yan sandan jihar Bauchi, Sufuritandan Ahmed Mohammed Wakil, ya shaida cewar harin ya wakana ne a yau Lahadi a kan babban hanyar Bauchi zuwa Jos wanda ya rutsa da jami’an da ke suntiri a daidai kauyen Nabordo.

Ya ce sakamakon harin sun rasa jami’insu na dan Sanda guda Inspector Mukhtar Ibrahim, 35 da kuma wani farar hula guda, Uba Samaila, dan shekara 33 mazaunin kauyen Nabordo, “Sun rigamu gidan gaskiya ne a asibitin ATBU yayin da suke amsar kulawar likitoci bayan harsasan da suka samesu.”

Wakil ya kara da cewa, “Yan sanda sun samu dawo da bindigar marigayin mai lamba NO.32486 sannan kuma an mika gawar mamatan ga iyalansu domin musu sutura kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar.

“Tunin aka kara tura jami’an tsaro yankin domin tsananta bincike don kamo wadanda suka aikata wannan danyen aikin”.

Yana mai cewa sun kuma yi kokarin dawo da doka da oda a yankin wanda jama’a ke cigaba da tafiyar da harkokin su na yau da gobe.

SP Wakil ya kara da cewa, “Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Bauchi, CP Sylvester Abiodun Alabi, ya nuna matukar kaduwarsa bisa wannan harin tare da mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu.

“Tuni CP Alabi ya nada umarnin kaddamar da bincike kan wannan lamarin”.

SendShareTweetShare
Previous Post

Sin Ta Kashe Yuan Biliyan 931.6 Don Bunkasa Aikin Ba Da Ilmi Tsakanin 2016-2020

Next Post

A Ceto Mana Naira Tiriliyan 3.4 Da Muka Zuba Don Sarrafa Shinkafar Gida – RIPAN

RelatedPosts

INEC Ta Fara Horas Da Shugabannin Harkar Zaɓe Kan ƙara Yawan Rumfuna

INEC Ta Fara Horas Da Shugabannin Harkar Zaɓe Kan ƙara Yawan Rumfuna

by Sulaiman Ibrahim
20 mins ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kan ta...

Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Zirin Gaza

Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Zirin Gaza

by Sulaiman Ibrahim
9 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Isra'ila ta ce ta kai harin bama-bamai...

Yadda Sojoji Suka Kashe Kwamandan ISWAP A Damasak

Yadda Sojoji Suka Kashe Kwamandan ISWAP A Damasak

by Sulaiman Ibrahim
10 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Wani babban kwamandan ISWAP, Bukar Gana (wanda...

Next Post
RIPAN

A Ceto Mana Naira Tiriliyan 3.4 Da Muka Zuba Don Sarrafa Shinkafar Gida – RIPAN

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version