Rabiu Ali Indabawa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

’Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sanda, Sun Yi Awon Gaba Da Bindigarsa

by Rabiu Ali Indabawa
January 20, 2021
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Garkuwa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe wani dan sanda mai suna Michael, sun raunata wasu ‘yan sanda biyu sannan suka yi awon gaba da bindigogi biyu na wadanda lamarin ya rutsa da su sun ce, lamarin ya faru a yammacin ranar Lahadi a Borokiri da ke cikin Karamar Hukumar Birnin Fatakwal, Jihar Ribas, ya jefa yankin cikin tashin hankali.

‘Yan sandan sun kasance a bakin aikinsu ne a kan mahadar Kyaftin Amangala da ke Borikiri lokacin da ‘yan fashin suka far masu. Wata majiya, wacce ta yi magana cikin karfin gwiwa, ta ce, kungiyar asiri da ke addabar yankin ne suka kaddamar da harin. Ya ce maharan sun shigo ta gefen tekun Orupolo ne suka bude wuta a kan ‘yan sandan.

samndaads

Majiyar ta ci gaba da cewa, ‘yan kungiyar asirin, wadanda ke da safarar haramtattun kayayyaki, da kuma tace danyen mai ba bisa ka’ida ba ne suka aikata hakan. Ya ce maharan na iya yin wannan aika-aikar ne bayan tursasawa da karbar kudi da ‘yan sanda suka yi a shingen binciken. Lokacin da aka tuntube shi, Jami’in Hulda da jama’a (PPRO), na Rundunar ’Yan sandan Jihar Ribas, SP. Nnamdi Omoni, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce kwamishinan ‘yan sanda, Joseph Mukan ya ba da umarnin gudanar da bincike don zakulo wadanda suka aikata laifin. Omoni ya ce: “Zan iya tabbatar da ci gaban inda aka kashe wani daga cikin mutanenmu. Kwamishinan ‘yan sanda ya ba da umarnin gudanar da bincike. Ba ni da masaniya game da masu aikata laifin da su ka dauke bindigogin ‘yan sanda. ”

SendShareTweetShare
Previous Post

’Yan Sanda Sun Cafke Wasu Da Ake Zargin ’Yan Kungiyar Asiri Ne A Legas

Next Post

Sun Daba Wa Abokin Zamansu Wuka Har Lahira A Legas

RelatedPosts

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

by Rabiu Ali Indabawa
3 days ago
0

Daga Ahmed Muh'd Danasabe, Lokoja Ranar Lahadi da ta gabata...

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

by Rabiu Ali Indabawa
3 days ago
0

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri Biyo bayan harin da mayakan Boko...

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

by Rabiu Ali Indabawa
3 days ago
0

Daga Musa Muhammad, Abuja An kammala dukkan shirye-shirye don fara...

Next Post
Abokin Zamansu

Sun Daba Wa Abokin Zamansu Wuka Har Lahira A Legas

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version