‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 4 A Ekiti
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 4 A Ekiti

bySadiq
3 years ago
Matafiya

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu matafiya hudu a hanyar Ekiti zuwa Oke Ako a karamar hukumar Ajoni (LCDA) a Jihar Ekiti. 

An ce matafiyan na komawa Ibadan, babban birnin Oyo, bayan sun halarci wani taro a Jihar Kogi.

  • Yekuwar Kai Hare-Hare Abuja: British Airways Ya Dawo Da Jigilar Fasinja Zuwa Abuja
  • An Dakatar Da Mu Don Mun Nemi Mukamin Alkalin Babbar Kotun Kebbi – Wasu Alkalai

Wata majiya ta shaida wa NAN cewa an sace matafiya ne a ranar Lahadi.

“Mutane hudun da aka sace suna dawowa ne daga wani taron da aka yi a Kogi zuwa Ibadan a kan hanyar Irele Ekiti da Oke Ako,” kamar yadda majiyar NAN ta ruwaito.

“Ba mu ji komai daga bakin ‘yan bindigar ba tun jiya kuma muna fatan za su tuntubi iyalansu, watakila don neman kudin fansa.”

A cewar NAN, Kehinde Abejide, shugaban al’ummar Irele-Ekiti, ya yi Allah-wadai da lamarin, ya kuma bukaci Biodun Oyebanji, gwamnan Ekiti da ya dauki matakan inganta tsaro a cikin al’umma.

“Wadannan mutane hudu suna komawa Ibadan ne lokacin da aka kai musu hari aka yi garkuwa da su da safiyar Lahadi, kuma ba mu ji komai ba tun lokacin da aka kwashe su zuwa,” in ji Abejide.

“Muna kuka muna rokon gwamnati ta taimaka mana a wannan yanki, amma ga dukkan alamu babu abin da ke faruwa, musamman idan aka yi la’akari da abubuwan da ke faruwa a cikin al’umma.

“Ko da yake a baya mun yi shirye-shirye m a nan dangane da tsaro, amma a banza.

“Bari in yi kira ga gwamnan Ekiti da ya yi wani abu cikin gaggawa kan rashin tsaro kafin a halaka mutanenmu da daukacin al’ummar Ajoni LCDA.

“Akwai bukatar samar da wasu jami’an soja a tsakanin Irele da Oke Ako, wanda za su taimaka wajen dakile duk wani harin da ‘yan bindigar za su iya kai musu, domin da alama suna cin gajiyar rashin tsarin tsaro a nan.”

Sunday Abutu, kakakin ‘yansandan Ekiti, ya ce zai yi tsokaci kan lamarin idan ya samu karin bayani.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara

Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version