'Yan Bindiga Sun Yi Yunkurin Mamaye Garin Safana Da Raunata 'Yan Sanda 2 - Yan Sanda
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Yi Yunkurin Mamaye Garin Safana Da Raunata ‘Yan Sanda 2 – Yan Sanda

byEl-Zaharadeen Umar
2 years ago
'Yan bindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta tabbatar da wani hari da ‘yan bindiga suka kai a garin Safana inda suka raunata mutane uku, mutum biyu daga cikin jami’an tsaro.

Kakakin rundunar ‘yansanda na jihar Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu, ne ya tabbatar da haka ga wakilin LEADERSHIP HAUSA a Katsina.

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Za Ta Fara Bai Wa Malamai Da Masu Unguwanni Alawus
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Ta Kaddamar Da Matasa ‘Yan Sa-Kai

Aliyu, ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun so mamaye garin na Safana a cikin dare da misalin karfe 6:00 na maraice inda suka zo ne da muggan makamai suka fara harbi kan mai uwa da wabi.

Sai dai a cewar sa, baturen ‘yan sanda na Safana ya shirya wata tawaga ta jami’an tsaro inda suka fatataki ‘yan bindigar daga garin Safana.

“A lokacin wannan ɗauki ba daɗi da ‘yan bindiga sun raunata jami’anmu guda biyu tare da wani mutum ɗaya wanda yanzu haka suna asibiti ana ba su kulawa ta musamman ‘ inji shi

Ya ƙara da cewa tuni jami’ansu, suka bazama domin kamo waɗanda suka kai wannan hari. Kuma tuni an fara bincike a kan lamarin.

A nasa ɓangaren, ɗan majalisar dokokin jihar Katsina mai wakiltar ƙaramar hukumar Safana wanda shi ne mataimakin kakakin majalisar Hon. Abduljalal Haruna Runka, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Honarabul Abduljalal Runka wanda ya ce ya zuwa yanzu komai ya lafa, sai dai ya tabbatar da cewa jami’an tsaro sun halaka ‘ yan bindiga da dama wanda sai nan gaba za a ji yawansu.

” Yanzu nan maganar da nake da kai, mun samu labarin cewa an yi wa ɓarayin daji ɓarna sosai, kuma hakan ya faru ne saboda jajircewar jami’an tsaro da kuma dakarun tsaro na ‘Community Watch Corps’

A cewarsa, babu labarin kashe ko mutum ɗaya, sannan ba su yi nasarar sace kowa ba, sai dai sun kutsa kai cikin wani shagon sayar da magunguna sun kwashe masa ciniki.

Kamar yadda Honarabul Abduljalal Runka ya tabbatarwa manema labarai, ya ce, ‘yan bindigar sun zo ne a kan mashina akalla talatin, amma a cikin ikon Allah jami’an tsaro sun fatatake su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Wasu Mazauna Abuja Sun Shiga Rumbun Ajiya Na Hukumar NEMA Sun Sace Kayan Abinci

Wasu Mazauna Abuja Sun Shiga Rumbun Ajiya Na Hukumar NEMA Sun Sace Kayan Abinci

LABARAI MASU NASABA

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version