Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

‘Yan Jihar Yobe Ku Sa Ido Kan Mutanen Da Ke Kwarara Daga Jihar Borno, In Ji ‘Yan Sanda

by Muhammad
February 5, 2021
in RAHOTANNI
2 min read
Hakkin

A Nigerian policeman stands guard as All Progressives Congress (APC) party supporters march towards the Independent National Electoral Commission Office in Port Harcourt during a demonstration calling for the cancellation of the presidential election in the Rivers State on March 29, 2015. Thousands of supporters of Nigeria's main opposition party demonstrated in the southern state of Rivers, calling for the cancellation of elections locally because of alleged irregularities. AFP PHOTO / FLORIAN PLAUCHEUR (Photo by FLORIAN PLAUCHEUR / AFP)

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela,

Rundunar `yan sanda a jihar Yobe ta bayyana cewa a halin yanzu sun yi rajistar sama da mutum 2,000 wadanda suka yo kaura zuwa jihar Yobe, tare da kira ga al’umma su ci gaba da sa ido dangane da yadda jama’a ke shigowa jihar daga garuruwan Gubio, Magumeri, Kaga da Kunduga na jihar Borno.

 

Rundunar ta sanar da hakan a sanarwar manema labarai mai dauke da sa hannun jami’inta na hulda da jama’a ASP Dungus Abdulkarim, a birnin Damaturu, ranar Alhamis.

Abdulkarim ya sanar da cewa, ga dukan alamu al’ummar sun kauro ne daga yankunan su na asali saboda yanayin matsalar tsaron da ta addabi garuruwan su.

 

Har ila yau, ya bayyana cewa mafi akasarin mutanen suna garuruwan Geidam, Tarmuwa, Gujba, Kuka Reta hadi da kauyukan Kasesa da Kalallawa da ke kusa da Damaturu.

 

A hannu guda kuma, Kakakin `yan sandan jihar Yobe, ta bayyana cewa haduran motoci sun ci rayukan mutane kimanin 147 a hanyoyin daban-daban a fadin jihar, a cikin shekarar 2020, a sanarwar da ta fitar ranar Alhamis.

 

Ya fara da bayyana cewa, “A kididdigar da muka gudanar ya nuna sama da haduran mota 200 ne suka faru a jihar, ta hanyar alkaluman da sashen kula da hadura na rundunar (Traffic Department) ya fitar; daga 1 ga watan Janairun 2020 zuwa yau.”

“A wadannan haduran mota 41, wanda hakan ya yi sakamakon mutuwar mutum 147 karin wasu da dama kuma sun samu raunuka.”

 

“Bugu da kari kuma, bincike ya nuna yadda gudun ganganci, tuki ba bisa ka’ida tare da taka dokokin tuki ne su ka yi ummul-haba’isan yawaitar haduran.”

 

Haka zalika kuma, Kakakin Rundunar `yan sandan, ya bukaci direbobi da duk masu ruwa da tsaki a fannin da cewa su rinka taka-tsan-tsan da kiyaye dokoki a lokacin tukin, tare da jan kunne ga duk wanda aka kama da take doka, zai dan-dana kudarsa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Matsayin Kananan Hukumomi A Matakin Cigaba Da kuma Tsaron Kasa

Next Post

Ba A Taba Yin Gwamnatin Da Ke Tausayin Talaka Kamar Ta APC Ba – Mustapha Saulawa

RelatedPosts

ACF

Kungiyar ACF Da Badakalar Jagoranci A Yankin Arewa

by Muhammad
15 hours ago
0

Daga Zailani Bappa, Al’ummar Arewa da dama za su tabbatar...

NLC

Mafi Karancin Albashi: Wata Kungiya Ta Yi Tir Da Kalaman NLC Akan Dan Majalisa Datti Babawo

by Muhammad
15 hours ago
0

Daga Bello Hamza, Wata kungiya mai zaman kanta mai suna...

Abduljabbar

Abduljabbar Bai Kai Darajar A Yi Masa Gangami Ba –Sheikh Khalil

by Muhammad
2 days ago
0

Ya Ce, Dalilin Da Ya Sa Sarkin Musulmi Ya Hana...

Next Post
Saulawa

Ba A Taba Yin Gwamnatin Da Ke Tausayin Talaka Kamar Ta APC Ba - Mustapha Saulawa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version