Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

’Yan Kallo Za Su Koma Shiga Kallo A Watan Mayu A Ingila

by Muhammad
February 24, 2021
in WASANNI
2 min read
Kallo

NANJING, CHINA - JULY 17: Premier League Asia Trophy - West Ham United v Manchester City (Photo by Fred Lee/Getty Images for Premier League)

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kimanin ‘yan kallon kwallon kafa 10,000 za su koma shiga filin wasa domin kallo daga tsakiyar watan Mayu a shirin da gwamnatin Ingila ke yi na kawo karshen dokar kulle a wani jawabi da gwamnatin kasar tayi a ranar Litinin.

Firai Minista, Boris Johnson ya sanar da matakai hudu da aka tsara domin janye dokar killace kai don gudun yada cutar korona sannan za a koma yin wasannin da suka hada da na kwallon kafa da kwallon golf da na tennis daga 29 ga watan Maris.

samndaads

Za kuma a cimma hakan ne idan har aka samu nasara kan allurar riga kafin annobar da tasirinta kafin a amince a dage dokar kullen gabaki daya a cewar Fira Ministan, wanda shima cutar ta taba kamashi a shekarar data gabata.

Za a bude wuraren shakatawa da na motsa jiki a rufaffen wuri da wuraren linkaya daga ranar 12 ga watan Afirilu sai dai ana ci gaba da gudanar da gasar Premier League ba tare da ‘yan kallo ba, sannan kuma ana yi wa ‘yan wasa gwaji a kowanne mako.

Amma daman tuni kungiyoyin kasar ta Ingila musamman wadanda suke buga gasar firimiya suka fara kira ga hukumomi a kasar dasu bayar da damar magoya baya su fara shiga fili domin samun kudaden shiga bayan da tattalin arzikin kungiyoyin gaba daya ya karye sakamakon annobar cutar Korona wadda ta dakatar da komai.

Kungiyoyi da dama dai sun karye sakamakon kamuwa da cutar Korona wanda hakan ya shafi kokarin manyan kungiyoyi kuma sannan yasa ba’a kashe kudi ba a kasuwar saye da sayar da ‘yan wasa guda biyu da aka bude a baya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Aka Raba Jadawalin Kofin Zakarun Afrika

Next Post

Dakatar Da Saida Layukan Waya Ya Kara Ruruta Wutar Rashin Aiki – Kwararru

RelatedPosts

PSG

Bambancin Tuchel Da Pochettino A PSG

by Muhammad
20 hours ago
0

Ranar Lahadi kungiyar kwallon kafa ta Monaco ta je har...

Yadda Aka Raba Jadawalin Kofin Zakarun Afrika

by Muhammad
22 hours ago
0

An hada kungiyoyi uku da suka taba lashe kofin zakarun...

Arsenal

Arsenal Ba Za Ta Iya Komai Ba A Kakar Bana –Paul Merson

by Muhammad
2 days ago
0

Tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal Paul Merson,...

Next Post
Layukan Waya

Dakatar Da Saida Layukan Waya Ya Kara Ruruta Wutar Rashin Aiki – Kwararru

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version