Yusuf Shuaibu">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

’Yan Kasuwa Sun Bukaci Gwamnati Ta Amince Su Gyara Matatun Man Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
December 21, 2020
in TATTALIN ARZIKI
3 min read
Matatun Man Nijeriya

Galveston, UNITED STATES: An oil refinery is pictured 22 September 2005 on Galveston Bay in Texas City, TX. Hurricane Rita threatens a large portion of the US oil and gas operations industry in the Gulf of Mexico and along the Texas coast just weeks after a devastating blow to the sector from Katrina. Oil producers and refiners were attempting to secure their facilities in the face of a storm that threatens about 27.5 percent of the industry, said Red Cavaney, president of the American Petroleum Institute. AFP PHOTO/Robert SULLIVAN (Photo credit should read ROBERT SULLIVAN/AFP/Getty Images)

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

’Yan kasuwan mai sun bayyana cewa, a shirye  suke su gyara matatun man Nijeriya wadanda suka kwashe shekara da shekaru ba sa aiki, sanna za su zuba kayyayakin aiki wanda cikin karamin lokaci za su farfado. Bangaren ‘yan kasuwan da suke sarar man daga wajen sari su suka bukaci gwamnatin tarayya da su bari ‘yan kasuwa su ja ragamar matatun mai na  kasar nan. An bayyana cewa, ‘yan kasuwan man  su taka mahimmiyar rawa wajen tara kudade domin a samu damar farfado da matatun man  kasar nan.

Matatunn mai na Nijeriya sun hada da na Kaduna da Fatakwal da Warri sun dauki tsawan shekara da shekaru da su tace danyan mai ba duk da irin kudaden da kamfanin mai na kasa (NNPC) yake kashewa a kan matatun. An dai fitar da wani rahoto a ranar 23 ga watan Nuwamna wanda ke nuna yawan kudade da aka kashe wa matatun, wanda ya kai na naira biliyan 81.41 tun daga watan Junairu har zuwa watan Agustan wannan shekara, amma har zuwa wannan lokaci matatun man ba su tace mai ko digo ba.

samndaads

Domin magance wannan lamari, ‘yan kasuwan man sun bayyana wa manema labarai a Abuja cewa, suna da damar da za su iya gyara matatun man tare da gudanar da kasuwancin  hadin gwiwa idan suka sami nasarar gyarawa.

“Ya kamata gwamnati ta kira ‘yan kasuwa ta mika musu jan ragamar matatan mai daya ko biyu tare da gudanar da kasuwancin hadin gwiwa domin matatun  man su ci gaba da aiki yadda ya kamata,” in ji shugaban kungiyar ‘yan kasuwan man ta kasa, Billy Gillis-Harry.

“Ya kamata mun dauki hanyar yadda za mu gyara farashin mai da kanmu, idan har matatun man mu suna aiki yadda ya kamata, to za a sami saukin farashin mai a cikin kasar nan.

“Ya kamata a bai wa ‘yan kasuwa  damar gudanar da matatan mai daya ko biyu, saboda muna da damar gyara matatunmu su ci gaba da aiki yadda ya kamata.

“A shirye muke mu hada kai da gwamnati da kamfanin NNPC wajen gudanar da kasuwancin matatun mai domin samun riba wanda za a raba a tsakanin mu.”

Ya kara da cewa, dukkan ‘yan kasuwan  man da ke cikin kasar nan abin da suke bukata bai wuce son gudanar ganin an gyara matatun mai ta yadda za su dunga aiki domin a samu saukin farashin mai a Nijeriya.

Gillis-Harry ya ce, “muna bukatar a ba mu matatun mai na Warri da na Fatakwal domin mu hada kai da gwamnati wajen farfado da matatun ta yadda za mu sami damar kayyade farashin mai da  kanmu.”

Ya ce,  ‘yan  kasuwan mai a shirye suke su saya wa gwamnati  kayayyakin da take bukata domin gyara matatun man.

“Idan gwamnati ta ba  mu damar mu saya za mu yi farin ciki wajen samo kudade, saboda za mu gudanar da kasuwancin hadin gwiwa a ko’ina a fadin duniya domin tabbatar da cewa tattalin arzikin kasarmu yana aiki yadda ya kamata,” in ji shugaban ‘yan kasuwan man Nijeriya.

“Saboda kowani lita daya na mai da aka siya ana danganta shi ne da dalar Amurka, sannan ba mu gudanar da tattalin arzikinmu da dala, muna gudanarwa ne da naira.

“Muna shigowa da kudaden kasashen waje a ko da yaushe a cikin harkokin tattalin arzikinmu, wannan  shi ne ya hana tattalin arzikinmu ci gaba.

“Wannan ne dalilin da ya sa ‘yan kasuwan mai ke bukatar gwamnati ta ba su damar gudanar da harkokin matatun mai saboda su ci gaba da aiki yadda ya dace.”

Lokacin da aka tambaye shi ko rage farashin mai da aka yi na naira  biyar zai kara kawo tallafin, Gillis-Harry ya bayyana cewa ba zai  kawo ba. Ya tabbatar da cewa, zamanin bayar da tallafi ya shude wanda ya sa abubuwa suka tsaya a haka. Ya kara da cewa, idan gwamnati ta dawo da bayar da tallafi, to shi zai kayyade yanayin irin tattalin arziki a cikin kasar nan.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Samar Wa Da Manoman Rogo Kasuwa, Cewar Nanono

Next Post

Nijeriya Ta Narkar Da Naira Tiriliyan 1.62 Wajen Shigo Da Mai A Wata Tara

RelatedPosts

Kwastom

Kwastom Ta Samu Harajin Naira Biliyan 518 A Apapa Cikin 2020

by Yusuf Shuaibu
2 days ago
0

Hukumar Kwaston ta Nijeriya reshen yankin Apapa ta bayyana cewa,...

Nijeriya

Nijeriya Ta Narkar Da Naira Tiriliyan 6.46 Wajen Biyan Bashi A 2020

by Yusuf Shuaibu
2 days ago
0

Ministar kudi da kasafi da tsare-tsaren kasa, Misis Zainab Ahmed...

Abuja Zuwa Kaduna

An Fara Sai-da Tikitin Jirgin Kasan Abuja Zuwa Kaduna Ta Yanar Gizo

by Yusuf Shuaibu
2 days ago
0

Hukumar  kula da tashoshin jiragen kasan Nijeriya (NRC) ta bayyana...

Next Post
Shigo Da Mai

Nijeriya Ta Narkar Da Naira Tiriliyan 1.62 Wajen Shigo Da Mai A Wata Tara

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version