'Yan Kasuwar Nijeriya Za Su Haɗa Hannu Da Gwamnatin Kaduna Wajen Bunƙasa Tattalin Arzikin Jihar
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Kasuwar Nijeriya Za Su Haɗa Hannu Da Gwamnatin Kaduna Wajen Bunƙasa Tattalin Arzikin Jihar

byShehu Yahaya
1 year ago
yan kasuwa

Ƙungiyar ‘Yan Kasuwa Ta Nijeriya ( MATAN) ta bayyana aniyarta ta haɗa Hannu da Gwamnatin Jihar Kaduna wajen bunƙasa tattalin Arzikin jihar ta bangarori daban-daban.
Bayanin hakan ya fito ne daga bakin shugaban kungiyar, Dakta Yahaya Muhammad Kyabo Fagge a Kaduna yayin ƙaddamar da matasa ‘yan jihar Kaduna waɗanda za su yi aikin tara kuɗaɗen haraji na kasuwanni domin sauƙaƙa wa gwamnati wajen ƙara bunƙasa hanyoyin samun kuɗaɗen shiga.

  • Zargin Tube Sarkin Musulmi: Kallo Ya Koma Sakkwato

 

Shugaban ya ce ƙungiyar (MATAN) ta haɗa Hannu da Gwamnatin tarayya a kan bunƙasa tattalin Arzikin ƙasa kamar yadda Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da shirin.

‘Mun ƙaddamar da irin wannan taro a Kudancin Nijeriya wanda yanzu ga shi mun shigo Kaduna domin ƙaddamar da shi Wanda aƙalla matasa sama da 2000 Dubu biyu za su samu aikin yi a matakai daban-daban, haka Kuma tattalin Arzikin Jihar Kaduna zai ƙara bunƙasa”

“A Nijeriya gwamnatin jihar Kaduna tana daga gwamnatoci da suka Samar da ci gaba cikin Shekara guda a bangaren ‘yan kasuwa da ilimi da Noma da sauran ɓangaren da suka shafi ci gaban Al’umma saboda haka wannan ƙungiyar tana alfahari da ta shigo Kaduna kuma ta ɗauki ‘yan Kaduna domin horas da su yadda za su taimaka wa jihar wajen bunƙasa tattalin arzikinta Baki ɗaya” inji shi.

A Nasa jawabin Shugaban kungiyar (MATAN) na Jihar Kaduna Alhaji Abdurahman Mohammed l, ya koka a kan yadda ake karɓar haraji amma baya shiga asusun gwamnati wanda a cewarsa hakan ya sanya Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da kwamiti tsakanin ƙungiyar ‘yan kasuwa da hukumar tara kuɗaɗen haraji ta ƙasa domin toshe duk wata hanya da harajin gwamnati zai zurare.

Ya ce kashi 80 cikin 100 na mutanen Nijeriya ‘yan kasuwa ne, hakan ya sanya Gwamnatin Kaduna Ta ware shaguna sama da guda 300 a kasuwar bacci da za ta rabawa ‘yan kasuwa masu sana’ar gwanjo domin bunƙasa kasuwancinsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Next Post
bankin duniya

Shugaban Bankin Duniya Ya Yi Tsokaci Kan Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version