Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

’Yan Kunar Bakin-Wake Sun Halaka Mutane A Kauyen Borno

by Tayo Adelaja
September 20, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri

Wasu yan kunar bakin-wake guda uku; biyu maza daya ta mace, wadanda ake kyautata zaton mayakan kungiyar Boko Haram ne sun tayar da bama-baman dake jikin su inda sama da mutane 13 suka rasa rayukan su, a kauyen Mashimari na yankin karamar hukumar Konduga, a jihar Borno.

samndaads

Wata majiya ta kut-da-kut daga yan sintirin kato-da-gora a jihar Borno ta shaidawa wakilin mu ta wayar tafi-da-gidan ka cewar yan kunar bakin-waken tada bama-baman dake jikin su ne jim kadan bayan karar harbin iskar da jama’ar kauyen suka ji, a kokarin su na kubuta da rayukan su.

Bayanan sun tabbatar da cewa harin ya faru ne a kusa da matsugunin yan gudun hijirar Mandarari, wanda aka kaiwa hari a cikin watan August, kwanan baya. Tare da bayyana cewa”da farko Boko Haram sun fara da bude wuta da kimanin karfe na safiya ranar litinin, a daidai lokacin da mazauna wannan kauyen ke kokarin gudu zuwa garin Konduga ne; shi ne dai yan kunar bakin-wake uku suka yi shigar-burtu a cikin su inda a haka suka Tatar da ababen fashewar da yake a jikin su”. Inji majiyar.

Injiniya Satomi ya kara da cewa “haka kuma baki dayan wadanda wannan ja’ifar ta rutsa dasu an kwashe su zuwa babbar asibitin Maiduguri, wadanda kuma al’amarin su baiyi tsanani ba an mika su asibitin Konduga domin duba su”.Ya bayyana.

Yayin da adadin da Bello Dambatta, jami’in bada agajin gaggawa na musamman dake garin Konduga lokacin da wannan al’amarin ya faru ya bayar ya sha babban dana shugaban hukumar agajin jihar Borno ya bayar. Dambatta ya shaidar wa manema labarai cewa mutane 15 ne suka rasa rayukan su, inda mutane 43 suka samu mabbantan raunuka., Dambat

Rundunar yan-sandan jihar Borno ta ta bakin mai magana da yawun rundunar; DSP ISuku Bictor, da faruwar wannan al’amarin tare da bayyana alkaluman wadanda suka rasa rayukan su da suka hada har da wani shahararren malamin addinin musulunci kuma babban limamin garin.

Mista Bictor Isuku ya bayyana cewa“jiya da safiyar ranar lahadi wasu yan kunar bakin-wake wadanda muke kyautata zaton yan ta’addan Boko Haram ne sun kai hari a kauyen Kurumari mai tazarar kilomita 14 a gabashin karamar hukumar Magumeri. Yayin da mutane hudu suka mutu ciki harda Limamin garin.

“Yayin da kuma a yau litinin, shima da safiyar ranar litinin da kimanin karfe 10 da miti 50, wasu karin yan kunar bakin-wake maza biyu da mace daya suka kai hari wurare daban dababan a kauyen Mashemari na karamar hukumar mulkin Konduga. Inda mutane 13 suka mutu kuma 16 suka samu raunuka a cikin harin”. Ta bakin mai magana da yawun rundunar tsaron.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Kallabi: Nasihar Wata Dattijuwa Ga Wata Uwa

Next Post

An Kiyasta Man Fetur Ya Tashi Zuwa Dala 56

RelatedPosts

Jami’an NIS Na Samun Horo A Kan Amfani Da Dokokin Shige Da Ficen ƙasa

Jami’an NIS Na Samun Horo A Kan Amfani Da Dokokin Shige Da Ficen ƙasa

by Sulaiman Ibrahim
7 hours ago
0

Shirin yaƙi da safarar bil’adama da fasa-ƙwaurin ‘yan gudun hijira...

‘Yan Nijeriya Mutum Miliyan 15 Na Shan Kwayoyi, Inji Buba Marwa

‘Yan Nijeriya Mutum Miliyan 15 Na Shan Kwayoyi, Inji Buba Marwa

by Muhammad
9 hours ago
0

Shugaban Hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun...

Katin Zama Dan Kasa

Nijeriya Ta Wajabta Wa Jami’an Diflomasiyya Mallakar NIN

by Sulaiman Ibrahim
15 hours ago
0

A jiya Lahadi Gwamnatin Tarayya ta shaida cewar, ya zama...

Next Post

An Kiyasta Man Fetur Ya Tashi Zuwa Dala 56

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version