‘Yan Nijeriya Miliyan 95 Za Su Yi Zabe A 2023 —INEC
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 95 Za Su Yi Zabe A 2023 —INEC

byYusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa ‘yan Nijeriya miliyan 95 ne za su yi zabe a 2023.

Ta kara da cewa ba dukkan wadanda suka yi rajisitan katin zaben da aka kammala a wannan makon za su samu damar jefa kuri’a.

  • NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69
  • Gwamnatin Gombe Ta Kafa Kwamitin Sayarwa Da Raba Takin Zamani Don Saukaka Wa Manoma 

Kwamishinan yada labarai na hukumar INEC, Mista Festus Okoye shi ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin gudanar da wani shiri a gidan talabijin na Arise Tb.

Okoye ya bayyana adadin yawan wadanda za su jefa kuri’a a zaben 2023, wanda adadinsu ya kai miliyan 95.

A cewarsa, akwai yuwuwar hukumar za ta cire da yawan wadanda suka yi rajistar daga kididdigar hukumar tare da hana su katin zabe saboda sun yi rajista fiye da guda daya.

Okoye ya tunatar da cewa na farko da na biyu na aikin yin rajistan, an cire fiye da kashi 46 na wadanda suka yi rajista daga kididdigar hukumar sakamakon yin rajistan fiye da guda daya.

Ya ce, “Abun takaice ne a ce an kammala yin katin zabe a yanzu, amma saboda za mu hada dukkan kididdigan wadanda suka amshi katin zabe da muka kammala a kwanan nan tare da amfani da na’urarmu mu cire wadanda suka yi rajista fiye da guda daya.

“Kamar yadda muka sanar, lokacin da muka kammala goje adadin wadanda suka ka yi rajista fiye da guda daya na farko da na biyun aikin rajistar, mun cire sama da kashi 46 wadanda suka yi rajista fiye da guda daya.

Domin haka, za mu yi haka a aikinmu na uku da na hudu domin goje wadanda suka yi rajista fiye da daya.

“Bayan haka, za mu yi hakan a dukkan bayananimu, saboda sashin na 19 (1) na dokar zabe na 2022, ta tilasta wa hukumar zabe ta bayyana wadanda suka yi rajistar zabe a dukkan wuraren yin katin zabe da ke kananan hukumomin Nijeriya guda 8,809.

“Muna tsammanin za a samu wadanda suka yi rajistar zabe guda miliyan 95, inda za mu lika hotunan sama da miliyan 20 a shafi guda dubu biyar a wadannan wuraren rajista, daga baya sai mu lika sauran da suka rage.”

Kwamishinan INEC ya kara da cewa ba dole ba ne a sake kara wa’adin yin rajistan zabe, saboda idan har aka kara, to zai shafi sauran wasu ayyukan na shirye-shiryen zaben 2023.

Ya ce, “Mun bayar da isasshen lokaci ga wadanda suka cancanci yin rajistan zabe, wanda muka bayar da tazarar yin rajistar har na tsawon watanni 13.

“Lokacin da muka kara wa’adin wata daya na yin rajistar zabe, sai da muka kara yin hayan ma’aikata a dukkan wuraren yin katin zabe, sannan mun kara wasu na’urori a dukkan cibiyoyin yin rajista da suka gudana.

Haka kuma mun kara lokacin yin katin zaben tun daga karfe tara har zuwa karfe biyar na yamma, ciki har da ranakun Asabar da Lahadi.

Amma abun takaicin shi ne, mun kammala wannan aiki a ce sai mun kara wani wa’adi, aikinmu na zabe muna tafiyartar da shi ne kamar yadda doka ta tanada. Idan muka kara wani wa’adin yin rajista, to zai shafi jaddawalin ayyukan zaben 2023.”

Kwamishinan ya cewa sun bai wa jama’a duk irin lokacin da suke bukata don mallakar katin zabe. A kan haka ya ce ba za su sake tsawaita lokacin yankar rajistar ba, lura da yadda lokaci ke kara kure musu.

INEC ta ce tana so ta mayar da hankali ne ga sauran ayyukan da ke kan jadawalin zaben na 2023, kuma dole sai ta rufe yankar katin ne za ta iya samun ci gaba.

A ranar 28 ga watan Yuni ne, hukumar zaben ta sanar da tsawaita lokacin yin rajistar zuwa ranar 31 ga watan Yulin 2022, bayan bukatar hakan daga bangarori daban-daban na kasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Next Post
Matsalolin Da Nijeriya Ke Fuskanta Yanzu Ya Zarce Na 2015 Kafin Zuwan Buhari – Sanusi Lamido

Matsalolin Da Nijeriya Ke Fuskanta Yanzu Ya Zarce Na 2015 Kafin Zuwan Buhari - Sanusi Lamido

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version