'Yan Nijeriya Sun Koka Da Kara Kudin Litar Mai
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Koka Da Kara Kudin Litar Mai

byKhalid Idris Doya
9 months ago
Mai

Matatar man Dangote da kungiyar dillalan Man Fetur a Nijeriya sun daura alhalin tashin farashin mai na baya-bayan nan da karuwar farashin danyen mai a kasuwar duniya, yayin da ‘yan Nijeriya suka koka da wannan karin.

‘Yan Nijeriya dai sun wayi garin ranar Juma’a da sabon karin kudin man fetur a fadin kasar nan, inda suka nuna hakan a matsayin koma-baya.

  • A Shirye Kasar Sin Take Ta Kyautata Dangantakar Tattalin Arziki Da Amurka
  • Yajin Aikin Likitoci Ya Tsayar Da Al’amura A Asibitocin Abuja

Matatar mai ta Dangote ta kara farashin manta daga naira 899.50 kan kowace lita zuwa naira 950, inda ke nuni da an samu karin naira 50 wato kaso 5.

Bayan hakan, gidajen mai kuma sun kara farashin da suke sayar da litar mai kama daga naira 970 da naira 1,150 daga naira 935 zuwa naira 1,100 a kan kowace lita.

A wata sanarwar da kakakin matatar mai ta Dangote, Anthony Chijiena, ya fitar, ya yi bayanin cewa an samu karin farashin danyen mai a duniyance daga dala 70 zuwa dala 82 kan kowace ganga.

Ya ce, “Matatar Dangote ta dauki kusan kashi 50 cikin 100 na farashin da ake samu a kasuwannin mai na duniya. Wannan ya faru ne saboda jajircewar da muka yi na samar da man da inganci da arha, da kuma mallakar matatar man da ‘yan Nijeriya ke yi, wanda ya kasance jigon ayyukanmu. Idan matatar Dangote za ta kai duk wani karin farashin danyen mai zuwa kasuwa, farashin dillalan man zai kai kusan naira 1,150 zuwa naira 1,200 kowace lita a wasu wurare, idan aka kwatanta da farashin na naira 970 a halin yanzu.”

Su ma a bangarensu, PETROAN, ta cikin sanarwar da kakakinta, Joseph Obele, ya fitar, shi ma ya daura alhalin karin da tashin farashin danyen mai a kasuwar duniya.

Da yake nakalto abun da shugaban kungiyar PETROAN, Billy Gillis-Harry, ke cewa, tabbas tashin farashin dayen mai a kasuwar duniya zai shafi tace mai a Nijeriya.

“Tabbas tashin da saukar farashin mai na shafan gidajen manmu. Kuma yana shafan kasuwancinmu ma.

“Ko da yaushe farashin da muka sayar da kayanmu na samu asali ne daga yadda muka saya. Don haka, ka da a zargi mambobinmu da karin kudin mai da ake fuskanta a halin yanzu,” ya shaida.

Sai dai kuma ‘yan Nijeriya da dama sun nuna matukar damuwarsu kan wannan lamarin. Farfesa Theophilus Ndubuaku, ya ce, sabon karin kudin mai tunin ya shafi farashin kayan abinci da kudin sufuri.

Suleiman Abubakar, mazaunin Abuja, ya ce kwanakin da ke gaba za su zama masu wuya ga al’ummar kasa sakamakon wannan karin kudin Lltar mai da aka samu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Yara 536,000 Ba Sa Zuwa Makaranta A Katsina – UNICEF

Yara 536,000 Ba Sa Zuwa Makaranta A Katsina - UNICEF

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version