‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

byKhalid Idris Doya
1 year ago
Lantarki

‘Yan Nijeriya sun yi fatali da shirin hukumar kula da harkokin wutar lantarki (NERC) na rage kudin wutar lantarki da suke yi a ajin A wato ‘yan ‘Band A’ daga kan naira 225 zuwa naira 206.8 kan wutan da suka sha na sa’a guda.

Kungiyar Kwadago na NLC da TUC da kungiyar kwastomomin da ke amfani da wutar lantarki da kungiyoyin farafen hula sun shaida wa jaridar Punch bukatarsu na a gaggauwa ta sake nazari kan karin kudin wutar lantarki.

  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa
  • Tsaron Yanar Gizo: TUC Ta Yi Barazanar Shiga Zanga-zanga A Nijeriya

Sanarwar sabon farin wutar da NERC ta yi na zuwa ne kwanaki 33 bayan da ta tsula karin farashin ga ‘yan rukunin ‘A’ daga kan naira 68 na kudin wuta da suke sha a sa’a guda zuwa naira 225, lamarin da ke nuni da cewa an kara kudin wuta da kaso 240.

Kan karin kudin, gwamnatin tarayya ta ce hakan zai ba ta damar samun rarar naira tiriliyan 1.5.

Bugu da kari, majalisar wakilai, kungiyoyin kwadago da na lauyoyi sun yi tir da karin kudin wutar lantarki da ya shafi sama da kwastomomi miliyan 1.9.

Majalisar wakilai ta yi kira ga NERC da ta janye shirinta na karin kudin wutar lantarki a fadin kasa, yayin da kungiyar kwadago ta bayar da wa’adin mako biyu da a sake nazarin karin kudin wutar lantarki cikin gaggawa.

Sai dai, ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, ya dage kan dole fa ‘yan kasa su amince da karin kudin, yana mai cewa idan zuwa nan da wata uku ba a aiwatar da karin farashin ba, to kuwa al’umman Nijeriya za su rasa wutan ma baki daya.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan lamarin, mataimakin shugaban kungiyar TUC, Tommy Etim, ya ce, “Ba zai yuwu a amince da hakan ba. Gaba daya muna son a janye batun karin kudin wutar nan.”

Shi ma ma’ajin kungiyar NLC, Hakeem Ambali, cewa ya yi, “Wannan lamarin ya kasance abun damuwa matuka ga kungiyar kwadago, muddin ba wai samun karuwar wuta aka yi ba, kowani irin karin kudin da aka yi na wuta ba abun lamunta ba ne.”

Shugaban kungiyar NACCIMA, Dele Oye ya ce kamfanonin rarraba wutar lantarki a Nijeriya ba su da dalilin da za su buga karji su yi karin kudin wutan lantarki. Ya ce akwai bukatar masu ruwa da tsaki su sa baki wajen ganin an janye batun baki daya.

Shugaban NACCIMA ya ce muddin ba a samu ra’ayin masu ruwa da suka hada da kamfanoni, ‘yan kasuwa, masu amfani da wuta da kungiyoyin fararen huda ba wajen tattauna yadda za a yi karin kudin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (1)

Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (1)

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version