Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

’Yan Sanda A Filato Sun Fara Farautar Wasu Masu Kashe Mutane

by Muhammad
February 18, 2021
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Rabiu Ali Indabawa,

A ranar Laraba Rundunar ‘yan sanda a Jihar Filato ta fitar da sanarwar fara farautar wasu ‘yan bindiga da suka kashe mutane hudu a Bassa dake Jihar Filato.

Rundunar ta yi alkawarin kamawa tare da hukunta wadanda suka yi kisan. Mista Edward Egbuka, kwamishinan ‘yan sanda (CP) a jihar, ya ba da wannan bayanin lokacin da ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai ranar Talata a Jos.

samndaads

Kwamishina ‘yan sandan ya tabbatar da kisan mutane hudu a kauyukan Rikwe-Chongu da Zirshe na Miango Chiefdom a Karamar Hukumar Bassa. A cewar Egbuka, lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da yamma. Ya ce har yanzu ba a kama mutane ba. Amma, ya ba da tabbacin cewa ana ci gaba da bincike kuma nan ba da dadewa ba za a cafke wadanda suka aikata wannan mummunan aiki.

Kwamishinan, wanda ya ce zaman lafiya ya dawo cikin jihar, ya nuna rashin jin dadinsa cewa an hargitse a cikin makonni shida da suka gabata tare da yawan kai hare-hare a Karamar Hukumar Bassa. “A da ana samun zaman lafiya a Filato, amma an samu matsala a cikin makonni shida da suka gabata. “Duk abin da muke yi shi ne mu tsaurara matakan tsaro kan lamarin tare da tabbatar da an samar da dawwamammen zaman lafiya cikin jihar.

A taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a ranar Litinin, Kwamishinan ya ce an yi shi ne domin nemo mafita mai dorewa ga ci gaba da samun tarnakin rashin tsaro a wasu sassan jihar. A nata bangaren, kungiyar Ci gaban Irigwe (IDA) ta yi Allah wadai da mummunan lamarin, tare da bayyana shi a matsayin “abin bakin ciki.”

A wata sanarwa da Sakataren yada labarai na kasa na IDA, Mista Dabidson Malison ya fitar, ya nuna rashin jin dadinsa tare da yin kira ga hukuma da ta kamo wadanda suka aikata kisan tare da sanya su fuskantar fushin doka. “Shugabancin na IDA ya yi bakin ciki, da nuna damuwa da ci gaba da faruwar wannan danyen aikin ba wai kawai ya nuna mugunta da shedanci ba ne har ma da rashin mutuntaka ga dan’Adam a kan mutanen Rigwe,” in ji shi.

Ya kuma ce: “An yi cikakken adalci don kawo karshen duk wata barna ta rayuka da dukiyoyi a kasarmu.”

SendShareTweetShare
Previous Post

’Yan Boko Haram Sun Halaka Soji Bakwai A Barikin Borno

Next Post

Babu Shirin Kara Farashin Mai – NNPC

RelatedPosts

Dan Majalisar Tarayya Ya Sabunta Katin Jam’iyyar APC A Funtuwa

Dan Majalisar Tarayya Ya Sabunta Katin Jam’iyyar APC A Funtuwa

by Muhammad
6 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Funtua  Dan majalisar Tarayya me wakiltar mazabar...

Sace Daliban Zamfara: Sarkin Musulmi Da Gwamna Tambuwal Sun Kai Ziyarar Jaje

Sace Daliban Zamfara: Sarkin Musulmi Da Gwamna Tambuwal Sun Kai Ziyarar Jaje

by Muhammad
6 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, kasa da awa goma sha biyu da...

miyagun kwayoyi

Masu Garkuwa Da Mutane Muggan Kwayoyi Suke Bukata Matsayin Kudin Fansa – NDLEA

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa Shugaba kuma babban jami’i na Hukumar...

Next Post
Farashin Mai

Babu Shirin Kara Farashin Mai – NNPC

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version