Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home JAKAR MAGORI

’Yan Sanda Sun Cafke ’Yan OPC Da Suka Kama Shugaban ’Yan Bindiga

by Muhammad
March 9, 2021
in JAKAR MAGORI
2 min read
OPC
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Rabiu Ali Indabawa,

’Yan Sanda sun damke ‘yan kungiyar OPC da su ka cafke Iskilu Wakilin Ayete . Ana zargin wadannan mutane da yin kisan-kai a wajen kama wannan mutumi . ‘Yan OPC sun ce Iskilu Wakilin Ayete ne shugaban ‘yan bindigan da ke Ibarapa. Jaridar The Nation ta ruwaito cewa jami’an tsaron sun cafke  wadanda su ka kama wannan mutumi da ake zargin cewa ya na garkuwa da mutane.

Ana zargin Iskilu Wakiliin Ayete shi ne shugaban ‘yan bindigan da su ke ta’adi a Ibarapa, Jihar Oyo. Rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta reshen Jihar Oyo, ta tabbatar da cewa ta cafke mutane uku daga cikin ‘ya ‘yan kungiyar OPC da su ka kama Wakiliin Ayete.

Jami’an ‘yan sandan sun ce an yi wa wadannan mutane tambayoyi a game da kisan kai da su ka yi a wajen yunkurin kama wannan mutumi da ake zargi da laifi. Mai magana da yawun ‘yan sanda na Jihar Oyo, Olugbenga Fadeyi, ya ce Kwamishinan ‘yan sanda, ya ba da umarnin a wuce da Iskilu Wakiliin Ayete zuwa asibiti.

Jawabin ya ce: “Jami’an ‘yan sanda su na sanar da jama’a cewa da kimanin karfe 9:00 na safe, an kama wasu mutane uku da daga baya aka gana cewa ‘yan OPC ne.” “Sun shiga yankin Kajola, a Ibarapa na jihar (Oyo), da nufin kama wani Bafullatanin mutumi, Wakili, wanda ake zargi da hannu a ta’adin da ake yi wa Yarbawa.”

‘Yan Sanda su ka ce da ‘yan OPC din su ka shiga gidan Wakili, sun banka wuta, hakan ya sa su ka kona wata Baiwar Allah wanda har yanzu ba a gane wacece ita ba.

Jawabin ya karkare da cewa: “A karshe duk wanda ya ke da wani abu da Iskilu Wakili ya kai kara a ofishin CID da ke Iyaganku, Ibadan, domin a gudanar da bincike.”.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

’Yan Sandan Ruwa Sun Kashe ’Yan Fashin Teku Hudu A Musayar Wuta

Next Post

Farfadiya Da Yadda Ake Maganinta

RelatedPosts

Wiwi

NDLEA Ta Cafke Masu Fataucin Mutane Da Kwayoyi Na Naira Miliyan 564 A Abuja

by Muhammad
2 weeks ago
0

Babafemi ya ce wanda ake zargin mai shekaru 40 da...

kama

Yadda Danuwana Ya Tilasta Min Aikata Miyagun Laifuka –Wanda Ake Zargi

by Muhammad
2 weeks ago
0

A ranar Litinin Rundunar yan sandan karkashin jagorancin DCP Abbaa...

An Haifi Wani Yaro Da Azzakari Uku A Irak

An Haifi Wani Yaro Da Azzakari Uku A Irak

by Muhammad
2 weeks ago
0

Likitoci a Iraki sun bayar da rahoton haihuwar wani jariri...

Next Post
Farfadiya

Farfadiya Da Yadda Ake Maganinta

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version