Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home JAKAR MAGORI

’Yan Sanda Sun Ceto ’Yan Mata Masu Ciki Yayin Da Aka Bankado Masana’antar Jarirai

by Sulaiman Ibrahim
March 17, 2021
in JAKAR MAGORI
2 min read
’Yan Sanda Sun Ceto ’Yan Mata Masu Ciki Yayin Da Aka Bankado Masana’antar Jarirai
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Rabiu Ali Indabawa

’Yan sanda a jihar Anambra sun gano wata masana’antar sarrafa jarirai da ke aiki a yankin Otolo Nnewi da ke Jihar. Wata sanarwa da Mohammed Haruna, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar ya fitar, ta ce an gano masana’antar jarirai wacce ake gudanar da ita a matsayin gidan karuwai yayin gudanar da bincike kan yunkurin yin garkuwa da wani karamin yaro dan shekara hudu da aka yi kwanan nan.
Majiyar LEADERSHIP A YAU ta tunatar cewa a ranar 11 ga Maris, akwai wani rahoto a hedkwatar rundunar da ke Nnewi, cewa wani yaro dan shekara hudu a makarantar St Joseph, Otolo Nnewi, yana dawowa daga Makaranta tare da ‘yan uwansa yayin da wasu maza biyu a kan babur ya kama yaron kuma ya ya tafi da shi. Duk da haka, wasu masu baburan hana sun ceto yaron tare da bin sahun wadanda suka kama a yankin Akamili Nnewi.
Haruna ya ce binciken farko ya nuna cewa wadanda ake zargin wadanda fusatattun mutane suka bubbuge su an tabbatar da mutuwar daya daga cikinsu, sun ce Gladys Nworie Ikegwuonu ce ta turo su, wacce a yanzu haka suke aiki tare da ita, kuma ita ke kula da masana’antar sarrafa jarirai da gidan karuwai inda take ajiye kananan yara mata. Sannan tana sa a yi musu ciki bayan sun haihu sai ta sayar da jariran ga kwastomomin da ke jira.
Mai magana da yawun ‘yan sandan ya bayar da sunayen mutanen biyu da aka cafke kamar haka; Abuchi Ani, mai shekaru 32, na Ohazora, jihar Ebonyi, da Emeka Ikegwuonu, mai shekaru 49, na Akabukwu, Nnewi, daga Jihar Anambra. Ya kuma bayar da sunayen ‘yan mata hudu masu ciki da aka kubutar da su, kwai; Chisom Okoye, ‘yar shekara 20, daga garin Mgbaneze Isu, yankin karamar Hukumar Onicha, dake Jihar Ebonyi. Sai kuma Chinecherem Clement, ‘yar shekara 18 daga garin Agbaebo Isu a karamara Hukumar Onicha, Jihar Ebonyi. Blessing Ogbonna, ‘yar shekara 21 daga garin Nkwagu Isu karamar Hukumar Onicha, Jihar Ebonyi. Blessing Njoku, mai shekar 21, yar asalin garin Mgbaneze Isu, a karamar Hukumar Onicha, Jihar Ebonyi, dukkan su suna dauke da juna biyu.
Haruna ya kara da cewa rundunar tana kara kaimi wajen cafke babbar shugabar ta su da ake zargi domin gurfanar da ita da sauran wadanda suka aikata laifin gaban kotu.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Bukaci Buhari Ya Ayyana Masu Garkuwa A Matsayin ’Yan Ta’adda

Next Post

CBN Ya Gabatar Da Sabbin Cajin Kudi Mai Amfani Da Lambar ‘USSD’

RelatedPosts

Wiwi

NDLEA Ta Cafke Masu Fataucin Mutane Da Kwayoyi Na Naira Miliyan 564 A Abuja

by Muhammad
2 weeks ago
0

Babafemi ya ce wanda ake zargin mai shekaru 40 da...

kama

Yadda Danuwana Ya Tilasta Min Aikata Miyagun Laifuka –Wanda Ake Zargi

by Muhammad
2 weeks ago
0

A ranar Litinin Rundunar yan sandan karkashin jagorancin DCP Abbaa...

An Haifi Wani Yaro Da Azzakari Uku A Irak

An Haifi Wani Yaro Da Azzakari Uku A Irak

by Muhammad
2 weeks ago
0

Likitoci a Iraki sun bayar da rahoton haihuwar wani jariri...

Next Post
Bankuna

CBN Ya Gabatar Da Sabbin Cajin Kudi Mai Amfani Da Lambar ‘USSD’

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version