Awwal Mu’azu">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

’Yan Sanda Sun Damke Wanda Ya Zagi Shugaba Buhari A Katsina

by Awwal Mu’azu
May 2, 2020
in LABARAI
8 min read
'Yan Sanda
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Rundunar ’yan sandan jihar Katsina ta samu nasarar cafke wasu mutum uku bisa wani faifan bidiyo da ke yawo a kafar sadarwa ta zamani, inda aka zagi Shugaban kasa, Muhammadu Buhari da Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari.

Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a ranar Laraba da ta gabata, ta bayyana cewa cikin wadanda aka kama, akwai wani dattijo mai kimanin shekara 70 a duniya, Lawal Abdullahi Izala, Bahajaje Abu da kuma Hamza Abubakar, wadanda dukkansu suna zaune ne Unguwar Gafai da ke cikin birnin Katsina.

Cikin sanarwar, wacce Kakakin rundunar, SP Gambo Isah ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa wasu masu kishin kasa ne suka jawo hankalin rundunar bisa wannan bidiyo da ke yawo, inda aka cusa ma Shugaban kasa da Gwamnan Jihar Kastina zagi, inda wani mai suna Lawal Abdullahi, da ake yi wa lakabi da “IZALA” ya yi zagin.

Sanarwar ta ce, Kwamishinan ’yan sandan jihar, Sanusi Buba ne ya bayar da umurnin a yi bincike kan lamarin, wanda binciken ne ya kai ga wannan kame da aka yi. “Da ake bincikensa, wanda ake zargin ya amsa laifinsa,” in ji sanarwar.

Wani bincike da muka gudanar ya nuna mana cewa, baya ga shi Lawal Dan Izala, sauran mutum biyun kuma ana zargin daya ne da laifin daukar bidiyon, daya kuma da laifin yadawa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Yanayin da Wasu ‘Yan Mata SuKa Tsinci Kansu  Sansanin ‘Yan Hijira A Borno

Next Post

Korona: An Tube Rawanin Wani Limami A Abuja

RelatedPosts

Jami’ar Tarayya Ta Gusau Ta Musanta Labarin Harin ‘Yan Bindiga

Jami’ar Tarayya Ta Gusau Ta Musanta Labarin Harin ‘Yan Bindiga

by Awwal Mu’azu
6 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Shugabannin Jami'ar gwamnatin Tarayya dake Gusau (FUG)...

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

by Awwal Mu’azu
10 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim An yi wa Shugaba Muhammadu Buhari da...

Mukabalar

Kotu Ta Dakatar Da Yin Mukabalar Sheikh Abduljabbar Da Malaman Kano.

by Awwal Mu’azu
16 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Wata kotu a Jihar Kano ta...

Next Post
Ababen More Rayuwa

Korona: An Tube Rawanin Wani Limami A Abuja

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version