Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home Uncategorized

‘Yan Sanda Sun Kubutar Da Mutum 15 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

by Muhammad
April 4, 2021
in Uncategorized
1 min read
Garkuwa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ta samu nasarar kubutar da mutum goma sha biyar daga hannun masu garkuwa a karamar hukumar Chikun, da ke jihar Kaduna, kamar yadda kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Mista Samuel Aruwan ya bayyana.

Aruwan ya bayyana hakan ne a cikin wata takarda da ya rabawa manema labarai jiya Juma’a,  a Kaduna. Aruwan ya ce, rundunar ‘yan sandan ta tabbatarwa da gwamnatin jihar Kaduna cewa ta samu nasarar kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su  din.

“Rundunar ‘yan sandan sun yi wa dajin da aka ajiye mutanen dirar mikiya, wanda ke karamar hukumar Chikun, wanda kuma a nan ne suka kwato wadanda aka yi garkuwar da su, kamar yadda ya ce.

Aruwan ya ce, bayan kuma wata musayar wuta da aka yi da masu garkuwar an sake kubutar da wasu mata guda uku a Rijiya Uku da ke yankin.

Matan da aka kubutar guda uku an yi garkuwa da su ne tun a cikin watan  Nuwamba 18, 2020  lokacin da masu garkuwa suka yi wa kauyensu dirar mikiya suka yi awon gaba da su.

”Tun daga wancan lokacin suke hannun masu garkuwar, har zuwa wannan loaci da Allah ya kawo karshen lamarin. Aruwan, ya ci gaba da cewa, rundunar ‘yan sandan ta dada samun karfin gwiwa na kara fadada ayyukanta don ganin cewa an ceto dukkan wanda ya fada hannun masu garkuwar .

A kaeshe gwamna Nasir El-Rufai ya yabawa rundunar jami’an tsaron da suka yi wannan aiki, sannan kuma ya kara tabbatar musu da goyon bayan gwamnati don ganin sun samu nasara.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Muke Ajiye Naira Miliyan 750 Duk Wata Ga Gwamnati – PTAD

Next Post

Ina Dab Da Kashe Kaina Saboda Kuncin Rayuwa – Ummi Zee Zee

RelatedPosts

Gwamnatin Kaduna Ta Yi Wa Karnuka 6,250 Allurar Rigakafin Cutar Rabis

Gwamnatin Kaduna Ta Yi Wa Karnuka 6,250 Allurar Rigakafin Cutar Rabis

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Daga Bello Hamza, Abuja Gwamnatin jihar Kaduna ta samu nasarra...

Caca

Caca: An Kashe Mutum Uku Akan Naira 50 A Imo

by Muhammad
1 week ago
0

Daga Rabiua Ali Indabawa, An bayar da rahoton kashe samari...

Shari'a

Ma’aikatan Shari’a Sun Tsumduma Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani  

by Muhammad
1 week ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Ma’aikatan shari’ar sun ce shawarar da...

Next Post
Ina Dab Da Kashe Kaina Saboda Kuncin Rayuwa – Ummi Zee Zee

Ina Dab Da Kashe Kaina Saboda Kuncin Rayuwa - Ummi Zee Zee

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version