Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Sanda Sun Musanta Rahoton Kai Hari Ofishinsu Na Shinkafi

by
8 months ago
in RAHOTANNI
1 min read
Shinkafi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta musanta labarin da ke cewa, an kai hari ofishin ‘yansanda da ke garin Shinkafi.

In za a iya tunawa, a ranar Alhamis din da ta gabata ce, aka samu rahoton cewa, ‘yan bindiga sun kai hari ofishin ‘yansanda, inda aka kwashi bindigogi da harsasai.

Jin yadda wannan labari ya yadu, rundunar ‘yansanda ta jihar Zamfara, ta fitar da wata sanarwa wadda jami’in hulda da jama’a na rundunar,SP Mohammed Shehu ya sa wa hannu, ya ce, rahoton da aka bayar a jaridar Daily Trust a shafi na 8, ta ranar Asabar 25, ga watan Satumba, 2021, ba gaskiya ba ne, domin babu wani kai hari da aka yi a ofishin ‘yansanda da ke Shinkafi ta jihar Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Ukraine Ya Haifar Da Karin Tsadar Kayan Abinci A Nijeriya —Rahoton NBS

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

Haka kuma, rahoton kai harin Shinkafi ba gaskiya ba ne. Gaskiyar abin da ya faru shi ne, ranar Juma’a da safe, ‘yanbindiga nasu yawa sun yi yunkurin kai hari Shinkafi, amma sai hadin gwiwar jami’an tsaro da aka jibge a garin ya hana su iya kawo wannan harin.

“Babu wani rahoto na kashe wani jami’in tsaro ko kuma ‘yanbindiga. Haka kuma babu wani rahoto da ke nuna cewa, ‘yanbindigar sun tafi da wasu,”

Kamar yadda ya ce, akwai cikakken tsaro a garin na Shinkafi,al’umma na cigaba da kasuwancinsu. Sannan kuma ana cigaba da daukar sabbin matakan tsaro wadanda za su taimaka wajen tabbatar da samun dorewar zaman lafiya a wannan yanki.

Ya ce, al’ummar wannan yanki sun yi mamakin yadda jaridar ta Daily Trust ta bayar da wannan labara, ba tare da jin ta bakin jam’an ‘yansanda ko jama’ar gari ba.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Jami’an Kwastam Sun Kwace Kayan Da Kudinau Ya Kai Naira Biliyan 41.4  A Kano Da Jigawa

Next Post

An Kama Ma’akacin Lafiya Da Ake Zargi Da Yi Wa ‘Yan Ta’adda Magani A Katsina

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Ukraine Ya Haifar Da Karin Tsadar Kayan Abinci A Nijeriya —Rahoton NBS

Rikicin Ukraine Ya Haifar Da Karin Tsadar Kayan Abinci A Nijeriya —Rahoton NBS

by
5 hours ago
0

...

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

by Abba Ibrahim Wada
2 days ago
0

...

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

by Abba Ibrahim Wada
2 days ago
0

...

Za A Murkushe Ta’addanci A Nijeriya Kafin Karshen 2023 – Sojoji

Za A Murkushe Ta’addanci A Nijeriya Kafin Karshen 2023 – Sojoji

by Sabo Ahmad
3 days ago
0

...

Next Post
Zargin

An Kama Ma’akacin Lafiya Da Ake Zargi Da Yi Wa ‘Yan Ta’adda Magani A Katsina

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: