Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

‘Yan Siyasa Na Kokarin Mayar Da Siyasar Gudu Baya — Falasko

by Tayo Adelaja
September 14, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Awwal Umar

Honarabul Murtala Abdullahi Falasko shi ne mataimakin jami’an hulda da jama’a na jam’iyyar APC a karamar hukumar Gudu ta jihar Sakkwato, a takaitaccen hirarsa da LEADERSHIP A Yau, ya ce matakin da ‘yan siyasa ke dauka a karamar hukumarsa kokari ne na mayar da hannun agogo baya a siyasan ce.

samndaads

Honarabul Falasko ya bayyana cewa: “Maganar gaskiya ba abu ba ne mai kyau, domin da ‘yan sisayar sun san abin da suke yi da ba akan dan majalisa za a yi zanga-zangar ba. Domin tun bayan kammala zabukan kananan hukumomi ashirin da biyu cikin kananan hukumomi ashirin da uku da muke da su, sannan mu jama’ar karamar hukumar Gudu da gwamnatin jiha ta gudanar da wannan zabukan amma ba a yi na karamar hukumarmu ba har yanzu kuma ba a ce mana komai ba mu kai biyayya ga shi kantoman riko da maigirma gwamna ya nada mana, da cibgaban suke so da gaske ya kamata ne ‘yan siyasar su tunatar da maigirma gwamna cewar har yanzu fa ba a yi zabe a karamar hukumarmu ba.

“Honarabul  Sani dan majalisar dokokin jiha mai wakiltar Gudu ko a majalisar tarayya yake abin da yake yi yanzu ya can-canci a yaba ma sa. Domin shi mutum ne marar tsoro kuma ya tsaya akan hakkin talaka, amma idan akwai wasu makiya ta bayan fage da ke son ganin bayan karamar hukumar Gudu ta ba zan yi musu ba, abin mamaki da takaici shi ne kujera daya da muke alfahari da shi a wannan majalisar ana mana zagon kasa a kansa.” In ji shi.

“Shawarar da ni ke baiwa jama’ar Gudu, kar su yarda da ‘yan a fasa kowa ya rasa, kar su yarda da masu kokarin gurgunta karamar hukumar mu. Sannan ina jawo hankalin gwamnatin jiha kan muhimmancin zaben karamar hukumar Gudu, dan mu ma muna da hakkin kamar kowani dan jihar Sakkwato, maigirma gwamna ya tausaya mana, ya ba mu damar mu ta siyasa mu ma mu taka na mu rawar ganin ga jama’ar mu.” In ji Falasko

SendShareTweetShare
Previous Post

Asusun Bai Daya Ya Yi Tasiri A Jihar Sakkwato —Turakin Isa

Next Post

Nafisa Abdullahi Ta Zama Jakadiyar LEADERSHIP A YAU

RelatedPosts

Hutun Kirsimeti

Gobarar Sakkwato: Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Tambuwal

by Muhammad
47 mins ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Kakkarfar tawagar Gwamnatin Tarayya ta jajantawa...

An Sace Jami’ar Yaɗa Labarun NIS Reshen Jihar Edo

An Sace Jami’ar Yaɗa Labarun NIS Reshen Jihar Edo

by Sulaiman Ibrahim
3 hours ago
0

Masu garkuwa sun yi awon gaba da jami'a mai magana...

Tsaro: Wasu Gwamnonin Nijeriya Na Ganawa Da Shugabannin Fulani Makiyaya

Tsaro: Wasu Gwamnonin Nijeriya Na Ganawa Da Shugabannin Fulani Makiyaya

by Sulaiman Ibrahim
4 hours ago
0

Yau gwamnonin yammacin Nijeriya ke gudanar da wani taro da...

Next Post

Nafisa Abdullahi Ta Zama Jakadiyar LEADERSHIP A YAU

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version