‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana

byAbba Ibrahim Wada and Sulaiman
1 month ago
Wasan Afirka

Tuni aka fara kakar wasa ta shekara ta 2025 zuwa 2026 ta gasar Premier League ta Ingila inda aka ci gaba a ranar Juma’a 14 ga watan Agustan wannan shekarar kuma mai kare kambu, kungiyar kwallon kafa ta Liberpool ce ta fara wasa a gida a wasan da ta doke kungiyar kwallon kafa ta Bournemouth da ci 3-2 a filin was ana Anfield dake birnin Liberpool.

 

Tauraron danwasan kasar Masar Mohamed Salah, shi ne gwarzon danwasan gasar kuma zai yi yunkurin lashe takalmin zinare na biyar yayin da zai fara buga wasa da sababbin ‘yanwasan da kungiyar ta saya da suka hada da Hugo Ekitike da Florian Wirtz da Jeremi Frimpong da Leon da Milos Kerkez.

  • Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?
  • Xi: Har Kullum Sin Za Ta Kasance Amintacciyar Abokiyar Huldar MDD

Wasu ‘yanwasan Afirka da dama sun samu komawa manyan kungiyoyi, akwai kuma wasu sababbi a gasar daga kasashen Kongo, da Morocco, da Mozambikue, da Senegal. A gefe guda kuma, ‘yanwasan nahiyar kusan 50 ne za su bar wasannin gasar zuwa gida domin karawa a gasar Kofin kasashen Afirka ta 2025 (Afcon 2025) da za a yi daga 21 ga watan Disamba zuwa 18 ga Janairu.

 

Ko Mbeumo zai dawo wa United da karsashinta?

Dan wasan dan kasar Kamaru Bryna Mbeumo ya zama abin tattaunawa kuma mafi tsada a ‘yanwasan Afirka lokacin da ya koma Manchester United kan fani miliyan 65 daga kungiyar kwallon kafa ta Brentford. Dan kwallon mai shekara 25 ya ci kwallo 20 a gasar da aka kammala da kuma bayarwa a ci bakwai. Manchester United na tsaka da sake gina kungiyar karkashin mai horarwa Ruben Amorim bayan gama gasar a mataki na 15, wanda shi ne mafi muni a tarihin kungiyar na Premier League.

Mbeumo zai fuskanci matsi nan take domin ya nuna kwarewarsa tare da Matheus Cunha da Benjamin Sesko wadanda duka kungiyar ta sayo a wannan kakar domin kara karfin ‘yanwasan gabanra da kuma kokarin ci gaba da zura kwallaye a raga duk da cewa bayan buga wasanni biyu a gasar firimiya har yanzu babu daya daga cikinsu da ya zura kwallo a raga.

Wani babban cinikin da aka yi shi ne wanda dan wasa Mohammed Kudus ya kawo karshen zaman shekara biyu da ya yi a kungiyar West Ham kuma ya koma Tottenham kan fan miliyan 55. Danwasan na Ghana ya taka rawa sosai a West Ham a kakar farko, amma bai yi kokari ba a kaka ta biyu saboda yadda ya yi fama da salon wasa na mai horarwa Graham Potter.

Irin kokarin da dan wasan mai shekara 24 din ya yi shi ne ya sa kungiyoyi da dama suka dinga nemansa, kuma yanzu Tottenham za ta so ya nemo wannan bajintar tasa domin taimaka mata a sabuwar kaka. Saboda samun damar buga gasar zakarun Turai ta Champions League na daya daga cikin dalilan da suka sa ya koma kungiyar Tottenham ta birnin London.

Yayin da tauraron danwasa Son Heung-Min ya bar kungiyar, da kuma James Maddison da ya ji rauni, Kudus zai iya zama mai muhimmancin gaske tun daga farkon kaka.

 

Ko Ait-Nouri zai taimaki Man City dawo da martabarta?

Bayan komawa mataki na uku da kuma kammala kakar 2024 zuwa 2025 ba tare da wani kofin kirki ba, Manchester City za ta danno da karfinta domin daukar kofi. Kungiyar ta shiga kasuwa da wurwuri domin daukar danwasan baya daga bangaren hagu Rayan Ait-Nouri, kuma danwasan mai shekara 24 ya fara buga mata wasa a gasar Club World Cup da ba ta je ko’ina ba. Dab wasan dan kasar Aljeriya ya koma Manchester City ne daga Wolbes a kan kudi fam miliyan 31.

Ait-Nouri ya nuna barazanar kai hari sosai daga gefensa duk da yadda Wolbes ta sha fama a kakar bara, inda ya ci kwallo hudu da kuma bayar da bakwai a zira a raga. Bayan ya samu wuri a Manchester City, tabbas mai horarwa Pep Guardiola zai so sabon mutumin nasa ya kara wuta wajen jawo kwallo daga baya zuwa gaba, sai dai bai taimakawa kungiyar ba a wasan da suka yi Rashin nasara a hannun Tottenham a ranar Asabar.

Adingra a Sunderland. Kungiyar Sunderland ta dawo buga gasar Premier League a karon farko tun 2017, kuma tuni ta karade kasuwar sayen ‘yanwasa, har ma ta sayi 11.

Shida daga cikinsu ‘yan Afirka ne. Ta kashe kudi mafi yawa a tarihinta fan miliyan 30 kan dan kasar Senegal Habib Diarra, da daukar Arthur Masuaku da Noah Sadiki ‘yan kasar Kongo, da dan Mozambikue mai suna Reinildo, da Chemsdine Talbi na Morocco.

Simon Adingra da ya ci kofin Afcon 2023 da kasarsa Ibory Coast na cikin mutanen da ya sauya sheka daga kudu zuwa arewaci bayan fara wasa 12 kacal a kakar bara. Yayin da yake cikin ‘yanwsan da suka san Premier League, dan kwallon mai shekara 23 zai so ya taimaka wa Sunderland ci gaba da zama a gasar.

Har yanzu West Ham za ta ci gaba da aiki da dan Afirka bayan ta biya fan miliyan 19 wajen daukar El Hadji Malick Diouf daga Slabia Prague.

Kociyan kungiyar Graham Potter ya ce dan wasan Senegal din mai shekara 20 yana da yunwar buga wasa da kuma buri mai yawa saboda haka za su taimaka masa wajen cika burinsa kuma West Ham United ce kungiyar da zai samu wannan damar.

Shima danwasan Kongo Aedel Tuanzebe zai so ya sake guje wa barin gasar ta Premier a karo na biyu bayan ya koma Burnley daga Ipswich Town. Ganin cewa sai a ranar 1 ga watan Satumba za a rufe kasuwar saye da musayar ‘yan kwallon, akwai ‘yanwasan Afirka da za su motsa a bana zuwa Premier.

Dan wasan Senegal da Chelsea, Nicolas Jackson ya samu izinin barin Chelsea a kasuwar nan, yayin da shi ma na Kongo Yoane Wissa ke shirin barin Brentford zuwa Newcastle United.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar
Wasanni

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Next Post
Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version