Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

’Yan Wasan Chelsea Su Na Son Lampard Ya Zama Kociyan Kungiyar

by
3 years ago
in WASANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Da yawa daga cikin ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Chelsea da kuma ragowar masu koyar  da kungiyar a yanzu suna fatan kungiyar ta dauki tsohon dan wasanta, Frank Lampard domin ya maye gurbin Mauricio Sarri, wanda zai koma Jubentus.

Sarri dai ya taimakawa Chelsea ta kammala kakar wasan data gabata a mataki na uku kuma ya lashe gasar kofin Europa da kungiyar sai dai duk da haka ya bayyanawa kungiyar cewa zai koma zakarun kasar Italiya wato Jubentus domin ya cigaba da koyarwa  a can.

Tun farkon fara rade radin cewa Sarri zai bar Chelsea aka fara tunanin Lampard shine wanda kungiyar yakamata ta nema domin zama kociyan kungiyar bayan daya kusa kai kungiyar Derby County gasar firimiya ta bana kafin suyi rashin nasara a hannun Aston Billa.

Labarai Masu Nasaba

Chiellini Ya Bar Juventus

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

Kamar yadda wani dan jarida, Dean Jones ya tabbatar da yawa daga cikin ‘yan wasa da masu taimakawa mai koyarwa suna son tsohon dan wasan ya koma domin koyar da ‘yan wasan Chelsea sai dai shugabannin kungiyar basu gama gamsuwa da kwarewar Lampard din ba.

Sai dai wasu daga cikin tsofaffin ‘yan waasan kungiyar irinsu John Terry sun bayyana cewa abune mai kyau kungiyar ta bawa Lampard aikin kungiyar sai dai kuma bai taba koyar da wata kungiya a gasar firimiya ba wanda hakan zai iya zama matsala a wajensu.

Lampard dai har yanzu yana da ragowar kwantiragin shekara biyu a kungiyar Derby County kuma a kwanakin baya ya bayyana cewa yana jin dadin aiki da kungiyar saboda haka idan bai samu wata kungiya a gasar firimiya ba zai cigaba da aiki da kungiyarsa.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Meunier Zai Koma Arsenal Daga PSG

Next Post

Har Yanzu APC Ce Mafi Karfi A Siyasar Najeriya, Cewar Wani Jigo

Labarai Masu Nasaba

Chiellini

Chiellini Ya Bar Juventus

by Abba Ibrahim Wada
6 hours ago
0

...

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

klopp

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

barcelona

Barcelona Ta Sa Hukumar La Liga Asarar Makudan Kudade

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

Next Post
Har Yanzu APC Ce Mafi Karfi A Siyasar Najeriya, Cewar Wani Jigo

Har Yanzu APC Ce Mafi Karfi A Siyasar Najeriya, Cewar Wani Jigo

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: