'Yansanda Sun Bankado Maboyar 'Yan Bindiga, Sun Cafke Mutum 6 A Nasarawa
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Bankado Maboyar ‘Yan Bindiga, Sun Cafke Mutum 6 A Nasarawa

bySadiq
3 years ago
Nasarawa

Rundunar ‘yansandan Jihar Nasarawa ta ce ta kai farmaki maboyar masu garkuwa da mutane a kauyen Kiguna da ke cikin garin Lafiya, babban birnin jihar, tare da cafke wasu mutane shida.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Maiyaki Muhammed-Baba, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da ya gabatar domin gabatar da nasarorin da rundunar ta samu daga farkon watan Janairu, a ranar Litinin a Lafiya.

  • Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci
  • Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

Muhammed-Baba ya ce, a ranar 12 ga watan Janairu da misalin karfe 4:00 na safe, jami’an ‘yan sandan da ke aiki da sashen Assakio, bisa ga bayanan da suka samu, sun kai samame maboyar tare da kama wasu mutane hudu.

“An kwato AK-47 guda daya a cikin gidan, sai kuma sauran makamai da aka kwato,” in ji shi.

Kwamishinan ‘yansandan ya kuma ce a ranar 13 ga watan Janairu, jami’an ‘yansanda daga wannan sashe sun kama shugaban kungiyar masu garkuwa da mutane.

Ya kara da cewa, tun daga farkon shekarar nan zuwa yau, ‘yansanda sun kama wasu mutane 21 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban.

Mohammed-Baba ya bayyana wadanda ake zargin sun hada da: ‘yan fashi 16, sai wasu da ake zargin barayin shanu ne guda guda bigu da masu satar babura guda biyu.

Ya lissafa abubuwan baje kolin da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin kamar: motoci hudu, makamai da shanu da sauransu.

Kwamishinan, ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

Sai dai ya ce galibin wadanda ake zargin sun amsa laifukan da suka aikata kuma suna taimaka wa ‘yansanda wajen gudanar da bincike.

Mohammed-Baba ya danganta nasarar da rundunar ta samu da goyon bayan jama’a da sarakunan gargajiya da sauran hukumomin tsaro da kuma kafafen yada labarai.

Don haka ya yi kira ga jama’a da su bai wa ‘yansanda sahihin bayanan da za su taimaka musu wajen rage yawaitar aikata laifuka a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
An Gurfanar Da Manoma 3 Kan Zargin Sace Wata Mata A Abuja

An Gurfanar Da Manoma 3 Kan Zargin Sace Wata Mata A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version