'Yansanda Sun Cafke 'Yan Fashin Daji 7, Sun Ceto Mutane 15
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashin Daji 7, Sun Ceto Mutane 15

byHussein Yero
3 years ago
Daji

Rundunar ‘yansandan Jihar Zamfara ta kama wasu mutane bakwai da ake zargi da aikata laifukan da suka shafi fashi da makami ciki har da mace mai kai wa ‘yan bindiga makamai.

Sannan sun samu nasarar kubutar da wasu mutane 15 da aka yi garkuwa da su bayan shafe kwanaki 50 a hannun masu garkuwan.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Yanke Wa Dan Takarar Gwamnan YPP Hukuncin Daurin Shekaru 42 A Akwa Ibom
  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Yanke Wa Dan Takarar Gwamnan YPP Hukuncin Daurin Shekaru 42 A Akwa Ibom

Kakakin Rundunar ‘Yansandan jihar, SP Muhammad Shehu, ne ya bayyana haka yayin da yake gabatar da wadanda ake zargin ga manema labarai a shelkwatar rundunar da ke Gusau a ranar Alhamis.

A cewarsa, an kama wasu mutane shida da ake zargi da laifin hada baki, da kuma tsoratarwa da karbar kudaden fansa a garuruwan yankin karamar hukumar Anka.

Wadanda ake zargin sun hada da, Jamilu Muhammad na kauyen Gadar Manya, Zayyanu Barmo na kauyen Manya Babba, Abubakar Usman na kauyen Mandau, Lauwali Girkau na kauyen Girkau, Sala Girkau na kauyen Girkau da Abubakar Yahaya na kauyen Tungar Mani.

“Mutane shidan da ake zargin ‘yan fashi ne da ke sanya haraji a kan al’ummar da suke a garuruwan da yin garkuwa da su, inda suka tara miliyoyin Naira ta hanyar asusun banki da suka kirkira don haka.

“Bayan an yi musu tambayoyi, duk wadanda ake zargin sun amsa laifinsu sannan suka bayyana cewa suna aika wa da sakon barazana ga kauyukan ko dai su biya kudi ko kuma a kai musu hari sannan kuma sun amsa cewa sun karbi miliyoyin Naira daga wasu al’ummomi biyar.

“Ana ci gaba da gudanar da bincike mai zurfi da nufin kamo sauran wadanda ake zargi da hannu a wannan aika-aika,” in ji kakakin rundunar ‘yansandan.

Kazalika, rundunar ta kuma kama wata mata mai matsakaicin shekaru mai suna Gaje Abdullahi, ‘yar kauyen Madaci da ke Jihar Katsina bisa laifin safarar makamai da alburusai zuwa ga wani shahararren dan bindiga da ake kira Dawa wanda ya addabi jihohin Zamfara da Katsina.

Sai dai matar a wata hira da manema labarai ta amsa laifin ta, inda ta ce Dawa ne ya tilasta mata aikata wannan aika-aika saboda tsoron kada su afka mata kamar yadda suka yi wa mijinta suka kashe shi tare da jimata rauni a fuska.

Gaje ta bayyana cewa, shi Dawa aikenta ya yi ta amso masa gyada kuma har ya yi mata alkawarin zai ba ta tiya goma dan yin Kulikuli kuma ya bata naira dubu goma kudin Mota, “Ashe harsashin ne ya aikeni amso ba gyada ba ce.”

Har-ila-yau, ‘Yansanda sun ceto mutanan dajin sabon garin Dustin Kaura da ke gundumar Danjibga a karamar hukumar Tsafe wanda ya kai ga ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Next Post
Shugaban Rikon Kwarya Na Chadi Na Son Zurfafa Hadin Gwiwa Tare Da Sin 

Shugaban Rikon Kwarya Na Chadi Na Son Zurfafa Hadin Gwiwa Tare Da Sin 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version