Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yansanda Sun Kama Mutum 19 Kan Zargin Ta’addanci A Abuja

by
4 months ago
in Kotu Da 'Yan Sanda
1 min read
Zargin
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Jami’an ‘yansanda da ke Abuja sun samu nasarar kame wasu mutum goma sha tara, da ake zarginsu da laifin garkuwa da mutane, da kisan kai da kuma wasu miyagun ayyuka. Kwamishinan ‘yansanda na Birnin tarayya, Abuja, Babaji Sunday, ya ce, mutum uku daga cikin wadanda aka Kaman ana zarginsu da laifin kashe Dakta Obisike Donald Ibe, mai kimanin shekara 37 wanda ke aiki a cibiyar binciken koda ta Zenith Lab, da abokinsa da wani abokin zamansa, Ezekiel Edoja dukkansu suna zaune a rukunin gidaje na Games da ke Abuja.

Wadanda ake zargi da aikata wannan laifi su ne, Abdulsalam Ibrahim da da Fidelis Ezekiel da Phillimon Hussaini. Wadanda ake zargin sun tabbatar da aikata wannan laifi, lokacin da ake bincikensu.

Kwamishinan ya ce, tun da suka samu wannan rahoton suka dauko gawarwakin kuma suka ci gaba da farautar wanda ya yi wannan danyen aiki.

Labarai Masu Nasaba

Budurwa Ta Maka Mahaifinta Kotu Kan Kin Aura Mata Masoyi

Malamin Islamiyya Ya Fada Tarko Bisa Mu’amala Da Matar Aure

Wanda ya aikata wannan aiki kuma ya gudu da wata mota da kuma wasu kudi kimanin dala 1,000, da wayar wannan likita da katin ATM. Kwamishinan ya ce, a cikin watan Janairu sun samu rahoto daga ofishinsu na Karu kan kashe wani manomi mai suna Mohammed Usman. Binciken da ‘yansanda suka yi, ya sa suka kama, Muhammed Abubakar, wanda kuma da kansa ya yi bayani a rubuce, cewa, shi ne, ya dabawa marigayin wuka kuma ya gudu, bayan wata sa-in[1]sa tsakaninsa da Daktan, sakamakon haka kuma ya mutu.

Haka kuma, a cikin watan Janairu ‘yansanda sun kama Shu’aib Usman da Sani Auwal. Sauran wadanda ake zargin su ne, Sani Auwal, wanda ake zarginsa da sa hannu wajen yin garkuwa, da kuma yunkurin koyawa wasu yadda za su yi garkuwa. Yanzu haka Auwal na tsare a hannun ‘yansanda, suna ci gaba da bincikensa.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

An Sace Wani Dalibin Jami’ar Bayero Da Ke Kano

Next Post

2023: Dattawan Arewa Sun Yi Tsayuwar Daka Kan ‘Yancin Takara

Labarai Masu Nasaba

Budurwa Ta Maka Mahaifinta Kotu Kan Kin Aura Mata Masoyi

Budurwa Ta Maka Mahaifinta Kotu Kan Kin Aura Mata Masoyi

by Sabo Ahmad
19 hours ago
0

...

Malamin Islamiyya Ya Fada Tarko Bisa Mu’amala Da Matar Aure

Malamin Islamiyya Ya Fada Tarko Bisa Mu’amala Da Matar Aure

by Sabo Ahmad
20 hours ago
0

...

Kisan

Adadin Kisan Da ‘Yan Bindiga Suka Yi A Watan Jiya

by Abubakar Abba
3 weeks ago
0

...

Kisan Kai

Ya Kashe Dan’uwansa Da Wuka Kan Iccen Girki A Jigawa

by Sabo Ahmad
4 weeks ago
0

...

Next Post
Arewa

2023: Dattawan Arewa Sun Yi Tsayuwar Daka Kan ‘Yancin Takara

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: